Zinedine Zidane ya ce Hazard yana burge shi

Asalin hoton, Inpho
Kocin Real madrid Zinedine Zidane ya ce a kodayaushe yana yaba wa da salon wasan Eden Hazard.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rohotonni ke alakanta dan wasan da komawa Real Madrid.
A baya dai dan wasan mai shekara 28 ya ce zai yi matukar wahala ya sabunta kwantiraginsa a Stamford Bridge, saboda yana mafarkin zuwa Madrid.
Kwantiragin dan wasan dai zai kare a watan yunin 2020, yayin da rahotonni ke cewa Chelsea na son sayar da shi a karshen kaka.
Zidane ya ce: "Dan wasa ne da koyaushe nake yaba masa saboda hazakarsa."
Zidane, mai shekara 46 ya dawo aikin horar da Real bayan da kungiyar ta sallami Santiago Solari a watan Maris, bayan da ya bar kungiyar a watan Mayun 2018 kwanaki biyar bayan lashe kofin Zakarun Turai na Champions League karo na uku a jere a kungiyar.
A yanzu dai Zidane, wanda kungiyarsa ke ta uku a kan teburin Laliga da ratar maki 13 tsakaninta da Barcelona wadda ke ta daya, zai mayar da hankali kan cinikin 'yan wasa idan an bude kasuwar sayayya.







