Man City ta yi wa Tottenham ruwan kwallaye

Asalin hoton, Getty Images
An wallafa
Manchester City ta lallasa Tottenham a wasan da suka yi gumurzu ranar Asabar inda suka tashi wasan 4-1.
Hakan yana nufin kungiyar ce za ta ci gaba da jan ragama a teburin gasar, inda take maki 52.
Sakamakon ya sa Tottenham ta koma matsayi na bakwai a teburin Gasar Firimiya da maki 31.
Sauran sakamakon wasannin da aka buga a gasar a ranar Asabar su ne:
- Leicester 0-3 Crystal Palace
- Arsenal 1-0 Newcastle
- Brighton0-0 Burnley
- Chelsea 1-0 Southampton
- Watford1-4 Huddersfield
- Stoke 0- 3 West Ham
Karanta wadansu karin labarai





