An sauya ranar da Arsenal ya kamata ta je gidan Newcastle

An wallafa

Mahukutan Premier League sun canja ranar da Arsenal ya kamata ta ziyarci Newacastle United a wasa na biyu a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Tun farko an tsara cewar Gunners za ta ziyarci St James Park ranar Asabar 6 ga watan Mayu, yanzu ya koma ranar Lahadi 7 ga watan Mayu.

Mahukuntan sun ce sun yi hakan ne domin haska wasan a talabijin, domin yana daya daga cikin wadanda sa suyi zafi a gasar Premier League a makon.

Kungiyoyin biyu sun kara a wasan farko a Premier ta bana a Emirates, inda suka tashi 0-0 ranar 3 ga watan Janairun 2023.

Arsenal wadda ta yi wasa 28 kawo yanzu, tana ta daya a kan teburi da maki 69 da tazarar takwas tsakaninta da Manchester City ta biyu, mai rike da kofin bara.

Newcastle tana ta biyar a teburin Premier Leage da maki 47, bayan da ta buga wasa 26.

Arsenal za ta karbi bakuncin Leeds United ranar Asabar 1 ga watan Afirilu a Emirates, sannan ta ziyarci Liverpool ranar 9 ga watan Afirilu.

Ita kuwa Newcastle United za ta karbi bakuncin Manchester United ranar Lahadi 2 ga watan Afirilu, sannan ta je gidan West Ham kwana uku tsakani.

Arsenal na kokarin lashe Premier League na bana a karon farko, tun bayan 2004, karkashin Arsene Wenger.

Sai dai kofin da take fatan dauka kenan a kakar nan, bayan da aka fitar da ita a Europa League da FA Cup, Manchester United ce ta lashe Carabao Cup.

Kofin farko da ta dauka kenan tun bayan 2016/17 karkashin Jose Mourinho, wanda ya dauki League Cup da Europa League.