Ilele ya sa Autan Mamman ya ruga da gudu sau biyu

An wallafa

Ilele Garkuwan mai caji daga Kudu ya dambata da Autan Mamman daga Arewa a damben Lahadi a gidan wasa da ke Marabar Nyanya jihar Nasarawa, Najeriya.

Sau biyu Ilele yana sa Autan Mamman na gudu a karawar da ba ta yi kisa ba a gidan wasa na Idris Bambarewa da ke karamar hukumar Karo a jihar Nasarawa, Najeriya.