Man City ta kawo karshen kasa cin wasa bakwai a jere a dukkan karawa

Manchester City

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Manchester City ta doke Nottingham Forest 3-0 a wasan mako na 14 a Premier League da suka kara a Etihad ranar Laraba.

Minti takwas da take leda City ta fara cin ƙwallo ta hannun Bernardo Silva, sannan Kevin De Bruyne ya kara na biyu tun kan hutu.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Jeremy Doku ya zura na uku a raga, kenan City ta haɗa maki ukun da take bukata.

Da wannan sakamakon City ta kawo karshen wasa bakwai a jere a dukkan fafatawa da ta kasa yin nasara.

Tun bayan da City ta ci Southampton 1-0 a Premier League ranar Asabar 26 ga watan Oktoba, daga nan ta jera wasa bakwai ba tare nasara ba a dukkan fafatawa.

Ranar 30 ga watan Oktoba Tottenham ta fitar da ita a League Cup, bayan da aka doke ta 2-1, irin sakamakon da ta yi rashin nasara kenan a Bournemouth ranar 2 ga watan Nuwamba a Premier League.

Daga nan City ta je ta kwaso 4-1 a Sporting a Champions League ranar 5 ga watan Nuwamba, sannan Brighton ta doke ta 2-1 a Premier ranar 9 ga watan Nuwamba.

Haka kuma dai City ta sha kashi a Etihad a hannun Tottenham a Premier 4-0 ranar 23 ga watan Nuwaba, sannan ta yi 3-3 da Feyenoord a Champions League ranar Talata 26 ga watan Nuwamba a gida.

Tun farko City ta zura uku a ragar Feyenoord a Etihad a gasar ta zakarun Turai daga baya aka farke saura minti 15 a tashi daga wasa.

Ranar Lahadi 1 ga watan Disamba, Liverpool ta yi nasara a kan City da cin 2-0 a wasan mako na 13 a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Ranar Asabar 7 ga watan Disamba, Crystal Palace za ta yi wa City masauki daga nan ƙungiyar Etihad ta je Juventus a Champions League ranar Laraba 11 ga watan Disamba.