KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 18/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 16 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Najeriya za ta kwaso ƙarin ƴan ƙasarta daga Afrika ta Kudu kan ƙyamar baƙi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Najeriya na shirin kwaso wasu ƙarin ƴan ƙasarta 83 daga Afirka ta Kudu, yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan ƙaruwa da zanga-zangar ƙyamar a ƙasar.

    Ana sa ran mutanen za su isa Legas ranar Laraba, inda wasu mutane masu zaman kansu suka ɗauki nauyin tikitin dawowarsu.

    Dawowar tasu na zuwa ne a lokacin da ƙungiyoyin masu zanga-zanga ke ci gaba da neman a fitar da baƙin da ba su da takardun zama, har ma suka sanya ranar 30 ga Satumba a matsayin wa’adin da suke son su fice daga ƙasar.

    Fiye da mutum 150 ne suka gudanar da zanga-zanga a Durban, suna kira ga ƙasashen yankin kudancin Afirka su magance matsalar ƙaura ba bisa ƙa’ida ba.

    Gwamnatin Afirka ta Kudu ta ce sama da mutum 80,000 ne aka kora ko kuma suka koma ƙasashensu da kansu yayin da take tsaurara matakan kula da shige da fice.

  2. EFCC ta gurfanar da wanda ake zargi da damfarar maniyyata aikin Hajji

    xxx

    Asalin hoton, EFCC/Facebook

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta gurfanar da wani mutum a gaban wata babbar kotun jihar Oyo bisa zargin shi da damfarar maniyyata ikin hajji naira miliyan 56.4.

    An gurfanar da mutumin ne kan zarge-zarge 57 wadanda ke da alaƙa da fashi da kuma yaudara.

    Hukumar ta lissafo sunayen wasu mutane 10 wadanda ta ce mutumin da take zargi ya damfara.

    Bayanin shari’ar da EFCC ta shigar ya nuna cewa mutumin ya karɓi kuɗin naira miliyan 56,491,000 daga mutane daga watan Nuwamban 2022 zuwa watan Yulin 2024.

    Mutumin ya riƙa shaida wa mutanen da yake karɓar kudi daga wurin su cewa shi jami’in hukumar kula da mahajjata ne ta jihar Kaduna.

    EFCC ta ce ya karɓi kuɗaɗen a hannunsu ne bisa hujjar cewa zai taimaka musu wajen tsara tafiyarsu zuwa aikin hajjin shekarar 2023.

    Hukumar ta ƙara da cewa mutumin ya ba su rasiɗin shaidar biyan kuɗi na ƙarya daga jihar Kaduna da kuma ƙasar Saudiyya.

  3. Iran ta ce ba za ta buɗe Hormuz ba har sai Amurka ta cika sharuɗɗan yarjejeniya

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya sake jaddada cewa Iran ba za ta buɗe Mashigar Hormuz ba har sai Amurka ta aiwatar da dukkan sharuɗɗan da ke cikin yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin ƙasashen biyu.

    Qalibaf ya ce Iran na buƙatar a cire takunkumin da aka ƙaƙaba mata, a saki ƙadarorinta da aka ƙwace, a kawo ƙarshen takunkumin man fetur, tare da dakatar da duk wata barazanar soja kafin a buɗe mashigar.

    Ya kuma yi gargaɗin cewa Iran a shirye take ta mayar da martani mai tsanani idan aka sake kai mata hari.

    Kalaman nasa sun zo ne bayan jami’an Rundunar Juyin Juya Halin Iran sun bayyana irin wannan matsayi, yayin da wa’adin kwanaki 60 da yarjejeniyar ta tanada ya ƙare ba tare da cimma cikakkiyar yarjejeniyar ba.

    A nasa ɓangaren, shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba ya sha’awar tsawaita yarjejeniyar wucin gadi da Iran.

  4. Malaman KASU kimanin 200 ne suka bar jami'ar - ASUU

    ...

    Asalin hoton, Uba Sani/X

    ƙungiyar malaman jami'o'i ta Najeriya (ASUU) reshen jami'ar jihar Kaduna (KASU) ta ce malaman jami'ar kimanin 200, ciki har da furofesoshi ne suka bar jami'ar sakamakon rashin kyawun yanayin aiki da kuma rashin aiwatar da yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta ƙulla da ASUU a 2025.

    Shugaban ASUU-KASU, Dakta Abubakar Abdullahi, ya bayyana haka a wani taron manema labarai ranar Litinin, inda ya ce mafi yawan malaman da suka fice sun samu aiki a sabbin jami'o'i da ke ciki da wajen jihar Kaduna.

    Ya ce rashin aiwatar da yarjejeniyar, wadda ta fara aiki tun watan Janairun 2026, ya sanya malaman KASU cikin mafi ƙarancin albashi tsakanin ma'aikatan jami'o'i a Najeriya.

    ASUU ta bai wa gwamnatin jihar Kaduna da mahukuntan jami'ar wa'adin makonni biyu su fara aiwatar da yarjejeniyar, tare da gargaɗin cewa rashin yin hakan na iya jawo yajin aikin sai baba-ta-gani a jami'ar.

  5. Kashi 40 cikin 100 ne na asibitoci suka da tsabta - MDD

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta ce kashi 40 cikin 100 ne kawai na cibiyoyin kiwon lafiya a duniya ke da banɗakuna masu tsabta da sauran muhimman kayayyakin tsafta da suka dace da marasa lafiya da ma’aikatan lafiya.

    A cikin wani rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da UNICEF suka fitar, an nuna cewa kashi 11 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya ba su da wata hidimar tsafta kwata-kwata, lamarin da ke shafar kusan mutum miliyan 936 a faɗin duniya.

    Rahoton ya kuma bayyana cewa akwai babban bambanci tsakanin yankuna, inda kashi 23 cikin 100 ne kawai na asibitocin da ke yankin Afirka ta kudu da Sahara ke da ingantattun ayyukan tsafta, idan aka kwatanta da kashi 55 cikin 100 a yankunan Tsakiya da Kudancin Asiya.

    Baya ga tsafta, rahoton ya ce kashi 85 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya suna da wadataccen ruwa, amma ƙasa da kashi 60 cikin 100 ne suka cika ƙa’idojin tsaftace muhalli da hana yaɗuwar cututtuka, musamman a ƙasashe masu ƙarancin ci gaba

  6. Iran ta musanta kai hari kan ofishin Barzani daga ƙasarta

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi ya ce babu wata shaida da ke nuna cewa harin da aka kai kan ofishin firaministan yankin Kurdistan na Iraq, Masrour Barzani, ya fito ne daga cikin ƙasar Iran.

    Araqchi ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da takwaransa na Iraq, Fuad Hussein, inda ya jaddada cewa Iran ba ta da wani bayani da ke nuna harin ya samo asali daga yankinta.

    A gefe guda, Fuad Hussein ya bayyana harin a matsayin wani abu mai haɗari da ka iya yin tasiri ga tsaron Iraq da ma yankin gaba ɗaya.

    Tun da safiyar ranar Talata, Masrour Barzani ya zargi Iran da kai harin jirgin maras matuƙi kan ofishinsa da kuma gidan shugaban hukumar leƙen asirin yankin Kurdistan.

    Shi ma mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya yi allawadai da harin, yana mai bayyana shi a matsayin wani lamari mai matuƙar tayar da hankali da ke buƙatar bincike da taka-tsantsan.

  7. 'Farin jinin Trump ya ragu matuƙa fiye da kowanne lokaci saboda yaƙin Iran'

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani sabon rahoto na kuri'ar jin ra'ayin jama'a da kamfanonin dillancin labaran Reuters da Ipsos suka gudanar ya nuna cewa farin jinin Shugaban Amurka Donald Trump ya ragu matuƙa zuwa kashi 33 cikin ɗari, mafi ƙanƙanta da ya taɓa samu tun bayan komawarsa mulki.

    Kuri'ar ta kuma nuna cewa yaƙin Iran na daga cikin manyan abubuwan da ke damun Amurkawa, inda kashi 80 cikin ɗari suka ce suna fargabar yiwuwar yaƙin Amurka da Iran ya daɗe.

    Sai dai kashi 33 cikin 100 ne kawai suka amince da yadda Trump ke tafiyar da mulki, yayin da kashi 64 cikin 100 suka bayyana rashin gamsuwarsu da salon jagorancinsa.

    Adadin amincewar da ake yi wa Trump ya ragu da kashi 35 cikin 100 da aka samu a farkon wannan wata, kuma ya yi daidai da mafi ƙarancin matakin farin jinin da ya samu a wa'adinsa na farko a watan Disambar 2017.

    Tun bayan da Trump ya ba da umarnin kai hari kan Iran tare da Isra'ila, farin jininsa ya ci gaba da raguwa sosai a bana.

    Yaƙin da Amurka da Isra'ila suka yi da Iran ya kuma haddasa rufe mashigar Hormuz, wanda ke da muhimmanci ga kasuwancin kusan kashi ɗaya cikin biyar na ɗanyen mai a duniya, lamarin da ya sa farashin man fetur ya tashi a Amurka.

  8. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta kasance da ku daga yanzu zuwa ƙarfe 4 na yamma in sha Allah.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.