Mece ce makomar Jami'ar Jihar Kaduna bayan malamai fiye da 200 sun bar ta?

Asalin hoton, Uba Sani/X
Wani jawabin da shugaban ƙungiyar Malaman Jami'a ta Najeriya, ASUU, reshen jihar Kaduna ya yi kan yawan malaman da suka bar jami'ar ya ɗauki hankalin ƴan Najeriya.
Cikin jawabin da ya gabatar a wani taron manema labarai, shugaban na ASUU reshen KASU, Dr Abubakar Abdullahi ya ce kimanin malaman jami'ar 200 ne suka daina aiki a cikinta, sakamakon abin da ya bayyana da rashin ingancin walwalar malaman.
Dr Abdullahi ya ce malaman da suka bar jami'ar sun haɗa da manyan malamai, ciki har da farfesoshi, lamarin da ya bayyana a matsayin babbar barazana ga ingancin koyarwa da bincike da ci gaban jami'ar gaba ɗaya.
ASUU ta danganta ajiye aikin malaman da abin da ta kira rashin kyawun walwala da kuma gazawar gwamnatin jihar Kaduna wajen aiwatar da wasu yarjejeniyoyi da suka shafi jin daɗin ma'aikata.
Dr Abdullahi, ya ce rashin aiwatar da yarjejeniyar da ƙungiyar ta cimma da gwamnatin tarayya a 2025 ne ya sa malamai da dama suka nemi guraben aiki a wasu jami'o'i da cibiyoyin ilimi da ke ba da yanayin aiki mai kyau da ƙarin albashi.
Masana ilimi sun ce barin ɗimbin malamai daga jami'ar na iya haifar da ƙarancin ƙwararrun ma'aikata da jinkirin gudanar da ayyukan ilimi da bincike da kuma ƙarin nauyi ga malaman da suka rage.
Waɗanne yarjejeniyoyi ne?

Asalin hoton, KASU
A hirarsa da BBC shugaban na ASUU reshen jami'ar, Dr Abubakar Abdullahi ya ce yarjejeniyoyin da aka cimma tsakanin gwamnati da ƙungiyar sun ƙunshi na walwalar malaman da kuɗaɗen gudanarwar makarantu.
''Yarjejeniyoyi ne suka ƙunshi kuɗaɗen gudanarwa da sauran haƙƙokin malamai ciki har da albashinsu'', in ji shi.
Dr Abdullahi ya ce tun bayan cimma waɗannan yarjejeniyoyi da gwamnatin tarayya, jami'o'i da dama na gwamnatin tarayya da na wasu jihohin sun fara amfana.
''Amma har yanzu jami'ar jihar Kaduna ba a fara amfana daga yarjejeniyar ba'', kamar yadda ya yi iƙirari.
Ya ƙara da cewa yarjejeniyar ta ƙunshi ƴancin cin gashin kan jami'o'i.
Dr Abdullahi ya ce rashin aiwatar da yarjejeniyar ya jefa rayuwar malaman jami'ar cikin mawuyacin halin tattalin arziki.
Malamai nawa ne suka bar jami'ar KASU?
Dr Abdullahi ya ce rashin aiwatar da wannan yarjejeniya ya jefa jami'ar jihar Kaduna cikin mawuyacin hali, lamarin da ya sa wasu daga cikin malaman jami'ar suka bar aiki a jami'ar.
''Wannan al'amari ya tailasta wa malaman jami'ar jihar Kaduna kimanin 200 barin aiki a jami'ar, saboda matsin tattalin arziƙi da suka shiga sakamakon rashin aiwatar da yarjejeniyar,'' kamar yadda ya shaida wa BBC.
Dr Abdullahi ya ce a yanzu malaman jami'ar da dama ba su iya ɗaukar ɗawainiyar sufurunsu domin zuwa wurin aiki.
''Na san malaman da ko kuɗin sanya mai a baburansu, ba su da shi, saboda ƙarancin albashin da ake biyan su'', in ji shi.
Wane hali jami'ar ta shiga?

Asalin hoton, KASU
Dr Abdullahin ya ce jami'ar ta shiga halin rashin ƙwararrun malamai, lamarin da ke barazana ga cigaban jami'ar.
''Shi ɓangaren ilimi ana buƙatar ƙwararrun masana da za su jajirce wajen tafiyar da ɓangaren, don haka tafiyar irin waɗannan malaman ya shafi harkokin ingancin koyarwa a jami'ar'', in ji shi.
Shugaban na ASUU ya ce hakan ba ƙaramar asara ba ce ga gwamnatin jihar da kuma jami'ar, saboda hakan koma-baya ne gare ta.
''A ƙa'idar jami'a shi ne yawan malaman da kake da shi ne zai yanke hukuncin yawan ɗaliban da jami'a za ta ɗauka, to in malamai na raguwa ai hakan zai shafi ingancin koyarwa a jami'ar'', in ji shi.
Mece ce buƙatar malaman KASU?
Dr Abdullahi ya ce babban abin da ƙungiyarsu ke buƙata daga ɓangaren gwamnatin jihar Kaduna shi ne aiwatar da yarjejeniyar da aka sanya wa hannu.
''Hakan ne zai sa malamai su samu albashi mai inganci, su kuma gudanar da ayyukansu yadda ya kamata ba tare da matsi ba'', in ji shi.
Ya ƙara da cewa idan hakan ta faru malaman jami'ar za su samu nutsuwar gudanar da ayyukansu.
Haka kuma shugaban na ASUU ya ce ƙungiyarsu na buƙatar gwamnatin jihar Kaduna ta bai wa jami'ar kuɗaɗen da suka kamata domin aiwatar da harkokinta.
''Sannan muna buƙatar gwamnati ta bai wa jami'ar ƴancin cin gashin kanta, wajen aiwatar da ayyukanta da take son gudanarwa a harabar jami'ar'', in ji shi.
Wace illa barin malaman zai yi wa jami'ar?
Dr Abdurrazak Ibrahim malami a Jami'ar North West da ke Kano, masanin harkokin koyo da koyarwar jami'o'i ya ce halin da Jami'ar jihar Kaduna ke ciki, yana buƙatar ɗaukar mataki.
''Bai kamata a bari Jami'ar Kaduna ta zama haka ba, domin jami'ar ita ce ta farko mallakin gwamnatin jiha a arewacin Najeriya, don haka bai kamata a bari ta shiga wannan hali ba'', in ji shi.
Masanin ya ce idan aka bari al'amura suka ci gaba da tafiya a haka a jami'ar Kaduna to komai zai iya taɓarɓarewa a jami'ar.
Ya ci gaba da cewa barin jami'a ga malamanta ba ƙaramar barazana ba ce, ga ci gaba da wanzuwarta.
''Ƙwararrun malamai ne da suka jima suna koyarwa shekara da shekaru, don haka rasa su ba ƙaramar illa ba ce ga jami'ar'', in ji shi.
Ya ƙara da cewa matsawar ba a magance wannan matsala ba, to za a iya rufe Jami'ar KASU.











