FA Cup: Man United za ta kara da ko dai Bristol City ko Nottingham Forest

An wallafa

Manchester United za ta fuskanci ko dai Bristol City ko kuma Nottingham Forest a zagaye na biyar a FA Cup cikin watan Fabrairu.

Kungiyar Old Trafford ta kawo wannan matakin ne, bayan da ta ci Newport County 4-2 ranar Lahadi.

Ita kuwa mai buga gasa mai daraja ta shida a Burtaniya, Maidstone United za ta kara da ko dai Sheffield Wednesday ko kuma Coventry City.

Mai buga National League, wadda ta fitar da mai buga Championship Ipswich Town a Portman Road tana cikin wadanda za su kara a zagaye na biyar din.

Mai rike da kofin, Manchester City za ta fuskanci mai buga Premier League Luton Town yayin da Liverpool za ta karbi bakuncin Watford ko kuma Southampton a Anfield.

Za a buga karawar zagaye na biyar a FA Cup tsakanin kungiyoyin ranar 26 ga watan Fabrairu.

Jadawalin zagaye na biyar a FA Cup.

  • Blackburn Rovers da Wrexham ko kuma da Newcastle United
  • Chelsea ko Aston Villa da Leeds United ko kuma da Plymouth Argyle
  • Bournemouth da Leicester City
  • Liverpool da Watford ko kuma da Southampton
  • Bristol City ko da Nottingham Forest ko kuma da Manchester United
  • Wolverhampton Wanderers da Brighton & Hove Albion
  • Sheffield Wednesday da Coventry City ko kuma da Maidstone United
  • Luton Town da Manchester City