Arteta ya ce hakkinsa ne ya kare Arsenal

Mikel Arteta

Asalin hoton, BBC Sport

An wallafa

Kocin Arsenal, Mikel Arteta ya ce "ya zama wajibi" ya kare kulob din bayan ya caccaki alkalin wasa a karawar da Newcastle ta doke su da ci 1-0 a ranar Asabar da ta gabata.

Ya ce shawarar da aka yanke kan kwallon Anthony Gordon a St James' Park "abin kunya ne" kuma "abin takaici".

Arsenal ta goyi bayan kalaman Arteta a wata sanarwa da kungiyar ta fitar, wadda tsohon dan wasan Manchester United Gary Neville ya kira abu "mai hadari".

"Ya zama wajibi gare ni in tsaya a gabanku in bayyana gaskiya ," in ji Arteta a ranar Talata.

"Aikina shi ne kare 'yan wasana da kuma kulob dina ta hanya mafi kyau, abin da nake da niyyar yi ke nan a kowanne lokaci.''

Rashin nasara a Newcastle ya kawo karshen wasan da Arsenal ta yi a gasar Firimiya ba tare da an doke ta ba, abin da ya sa ta zama ta hudu, inda akwai maki uku tsakaninta da Manchester City da ke jan ragamar teburin.

A ranar Laraba ne Gunners za ta karbi bakuncin Sevilla a gasar zakarun Turai a rukunin B.