Argentina ta dare matakin farko a Fifa ta yi kasa da Brazil

Asalin hoton, Getty Images
Argentina ta koma ta daya a kan jadawalin kasashen da ke kan gaba a taka leda a duniya da Fifa ta sanar.
Karon farko da Argentina ta hau kan wannan matakin tun bayan shekara shida, wadda ta lashe kofin duniya a Qatar a 2022.
Argentina ta samu wanan ci gaban bayan nasara biyu a wasan sada zumunta da ta ci Panama da Curacao, ita kuwa Brazil rashin nasara ta yi a hannun Morocco.
Faransa, wadda ta doke Netherlands da Jamhuriyar Ireland a wasannin neman shiga Euro 2024 ta koma ta biyu.
Brazil wadda take matakin farko ta koma ta uku, Ingila wadda ta ci Italiya da Ukraine tana ta biyar da Sifaniya a jerin 'yan 10 farko.
Jerin goman farko a Fifa
1 Argentina Argentina
2 France
3 Brazil
4 Belgium
5 England
6 Netherlands
7 Croatia
8 Italy
9 Portugal
10 Spain
Super Eagles wadda Jose Pesseiro ke jan ragama ta yi kasa ajadawlin kungiyoyin da ke kan gaba a taka leda a duniya.

Asalin hoton, Super Eagles
Najeriya wadda ta je ta ci Guinea Bissau 1-0 a watan jiya a wasan cikin rukuni a neman shiga kofin Afirka tana ta 40 a duniya, wadda take ta 35 a Disamba.
A nahiyar Afirka kuwa Super Eagles wadda take ta biyar a baya yanzu Masar ta karbi gurbin, Najeriya ta yi kasa zuwa ta shida.
Itama Kamaru ta yi kasa daga mataki na hudu a baya yanzu tana ta bakwai a Afirka.
Jerin 10 farnfo a tamaula a Afirka
- Morocco
- Senegal
- Tunisia
- Algeria
- Masar
- Najeriya
- Kamaru
- Ivory Coast
- Burkina Faso
- Mali











