Zidane: Idan mun yi nasara a yabe ni idan mun fadi a soke ni

Zinedine Zidane

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Real Madrid za ta kara da Osasuna ranar Laraba da kuma Atletico ranar Asabar
An wallafa

Yayin da Real Madrid ke shirye-shiryen karawa da Osasuna a La Liga wasan mako na 6, Zinedin Zidane ya amsa tambayoyi kan halin da tawagar tasa take ciki da kuma zamnsa a Madrid din.

Kungiyar tana kokarin dorawa ne kan nasarar da ta samu a Sevilla a ranar Lahadi, kuma Zidane ya ce "idan muka samu nasara a yabe ni idan kuma aka ci mu a soke ni".

Zidane yana wannan magana ne a taron manema labarai gabanin wasan da Madrid za ta karbi bakuncin Osasuna a ranar Laraba.

"Abin ba ya damuna, haka yake kullum. Wajibi ne mu mayar da hankalinmu kan wasanni kuma abin da nake yi kenan," in ji Zidane.

Yanzu haka Barcelona tana mataki na takwas a teburi bayan rashin nasara a hannun Granada ranar Asabar, sai dai kocin Madrid din kauuce wa magana kan halin da abokan hamayyarsu ke ciki.

"Abin da ke faruwa yanzu da Barcelona zai iya faruwa da Atletico Madrid. Abin da ya kamata mu yi shi ne, mu yi bakin kokarinmu wajen cin maki mai yawa.

"Mu saka dukkanin kwarewarmu a cikin fili kuma 'yan wasana su ne mafiya kwarewa."

Wasannin Real Madrid biyar na gaba:

Laraba 25 ga Satumba: Real Madrid 8:00 Osasuna - La Liga

Asabar 28 ga Oktoba: Atletico 8:00 Real Madrid - La Liga

Talata 1 ga Oktoba: Real Madrid 5:55 Club Bruges - Champions League

Asabar 5 ga Oktoba: Real Madrid 3:00 Granada - La Liga

Asabar 19 ga Oktoba: Mallorca 20:00 Real Madrid - La Liga

Teburin La Liga:

Teburin La Liga