Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Antonio Rudiger: Rudiger zai ci gaba da wasa a Chelsea in ji Thomas Tuchel
Kocin Chelsea, Thomas Tuchel ya ce yana da ''tabbacin'' cewar mai tsaron baya, Antonio Rudiger zai sa hannu kan yarjejeniyar ci gaba da taka leda a kungiyar.
Mai shekara 28 dan kwallon Jamus yana da damar tattaunawa da wasu kungiyoyin tun daga yanzu, bayan da kwantiraginsa zai kare a Stamford a karshen kakar 2021-22.
Rudiger ne ya ci kwallon da Chelsea ta doke Tottenham 1-0 a wasa na biyu a Caraboa Cup ta kuma kai zagayen karshe da ci 3-0 gida da waje.
Rudiger wanda ya buga wasan karshe a Champions League da Chelsea ta doke Manchester City 1-0, ana ta alakanta shi da zai koma ko dai Paris St-Germain ko Real Madrid ko Bayern Munich.
Ya kuma je Chelsea kan fam miliyan 29 daga Roma a Yulin 2017, wanda ya lashe FA Cup da Europa League da kuma European Super Cup a kungiyar ta Stamford Bridge.
Chelsea za ta buga wasan karshe da duk wadda ta yi nasara a wasan da za a buga ranar Alhamis tsakanin Liverpool ko Arsenal ranar 27 ga watan Fabrairu a Wembley.
Kungiyar Stamford Bridge tana ta biyu a teburin Premier League ta bana da tazarar maki 10 tsakaninta da Manchester City wadda ke jan ragama.
A makon jiya Tuchel ya ce ya yadda da dan wasa Rudiger, kuma baya ganin batun tsawaita yarjejeniyar dan kwallon a Chelsea da wata matsala.