Champions League: Man City za ta kara da Borussia a Hungary

Asalin hoton, Getty Images
Manchester City za ta buga wasan zagaye na biyu a Champions League da Borussia Monchengladbach a Hungary.
Hakan ya biyo bayan da gwamnatin Jamus ba ta amince da aka buga wasan a kasarta ba, saboda gudun yada cutar korona.
Jamus ta hana a shiga kasarta musamman ta jirgin sama ga kasashen da cutar korona ke kara yi wa ta'adi ciki har da Burtaniya.
Borussia za ta karbi bakuncin City a wasan farko a matakin gidanta ranar 24 ga watan Fabrairu a Fuskas Aarsena da ke Budapest a fafatawar kungiyoyi 16 da suka rage a gasar ta bana.
Shi ma wasan da Liverpool ya kamata ta fafata da RB Leipzig a Jamus za a yi shi a Hungary.
Kungiyoyin biyu za su kara ranar 16 ga watan Fabrairu, sannan Liverpool ta karbi bakuncin wasa na biyu.
Manchester City za ta yi wa Borussia masauki a fafatawa ta biyu ranar 16 ga watan Maris.







