Pillars ta hada maki uku a gasar Firimiyar Najeriya

Asalin hoton, Npfl
An wallafa
Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta yi nasara a kan FC Ifeanyi Ubah da ci 1-0 a wasan mako na goma a gasar cin kofin Firimiya Najeriya ranar Lahadi.
Pillars wadda take da kwantan wasa daya ta ci kwallon ne ta hannun Mustapha Musa a fafatawa da suka yi a filin wasa da ke Kofar Mata a Kano,
Da wannan sakamakon Pillars wadda ta yi 1-1 a Heartland ranar Laraba, yanzu tana da maki 13 kenan.
Sauran sakamakon wasannin mao na 10 da aka fafata kuwa:
- Nasarawa Utd 1-0 Heartland
- Rivers Utd 2-1 Sunshine Stars
- Plateau Utd 1-0 Wolves
- Lobi 1-0 Katsina United
- Kwara Utd 1-0 Rangers
- MFM 2-0 Adamawa Utd
- Dakkada 0-1 Akwa Utd
- Wikki 1-1 Abia Warriors







