Klopp bai jagoranci atisayen Liverpool ba

An wallafa

Kungiyar Liverpool ta sanar da cewar kocinta Jurgen Kloop bai ja ragamar atisaye ba a ranar Laraba, bayan da aka kai shi asibiti sakamakon rashin lafiya.

Likitoci sun duba Kloop mai shekara 50, domin tabbatar da cewar lafiyarsa kalau a matakin riga kafi.

Liverpool ta ce a yammacin Laraba zai koma gida, idan likitocin sun tabbatar da koshin lafiyar kocin.

Sai dai kuma Klopp zai bukaci a ci gaba da duba koshin lafiyarsa lokaci-lokaci.

Liverpool tana ta biyar a kan teburin Premier za kuma ta kara da Southampton a ranar Asabar a gasar Premier a Anfield.