Tankar mai ta kashe mutane da dama a Najeriya

Asalin hoton, na
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya, NEMA, ta tabbatar da cewa ta gano gawarwakin mutane casa'in da biyar yayainda wasu mutanen goma sha takwas ke kwance a asibiti sakamakon kama wutar da wata tankar mai ta yi yayin da mutanen kauyen Okobe a Jihar Rivers ke kokarin kwasar mai.
Hukumar ta NEMA ta kuma bayyana cewa al'amarin ya kuma shafi kananan motoci guda biyu.
Motar tankar dai ta yi hadari ne a kauyen na Okobe da ke karamar hukumar Ahoada.
Rahotanni sun ce jami'an 'yan sanda, da na 'yan kwana-kwana, da na NEMA na cikin ma'aikatan da ke yunkurin ceto wadanda al'amarin ya rutsa da su.
Ba wannan ba ne karo na farko da mutane suka rasa rayukansu a Najeriya ta hnayar tashin wuta yayin da suke yunkurin kwasar mai ko dai daga tankar da ta yi hadari ko kuma a bututan man da suka fashe.








