Mamakon ruwan sama ya kashe mutum 28 a Pakistan

Asalin hoton, EPA
Ruwan sama kamar da bakin-kwarya gami da tsawa ya ɗaiɗaita al'umma a Pakistan, inda ya kashe mutum 28 zuwa yanzu.
Aksarin waɗanda suka mutu mazauna Lardin Khyber Pakhtunkhwa ne.
Mamakon ruwan ya haddasa ambaliyar ruwa da lalata gwamman gidaje, an dinga nuna hotuna da ke nuna rufin gidaje fayau da faɗuwar gine-gine.
Sama da mutum 140 aka kƙiyasata kawo yanzu sun jikkata.
An kuma samu wasu da suka rasa rayukansu a yankin Punjab.
Masu aikin ceto sun bazama yankunan da ambaliyar ta afka wa domin taimaka wa mutane.
