Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata cewa sojoji sun zubar wa mata ciki a asirce

Wannan shafin yana kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta dama wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Aisha Bappa

  1. An harbe mata uku a wajen shan gahawa a Italiya

    Mata

    Asalin hoton, GIORGIA MELONI/FACEBOOK

    Wasu mata uku ciki har da aminiyar sabuwar firaiministar Italiya aka kashe bayan wani mutum ya bude wuta a wani wajen shan gahawa a birnin Rome na Italiya.

    An raunata wasu mutum hudu a wajen.

    Mutanen da ke cikin wajen na gudanar da taro ne a kan abin da ya shafi unguwarsu a lokacin da mutumin ya bude musu wuta.

    Magajin garin Rome, Roberto Gualtieri, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, sannan kuma zai kira taron gaggawa a kan lamarin.

    Yanzu haka mutumin da ake zargi mai kimanin shekara 57, na tsare kuma rahotanni sun ce dama can yana da matsala tsakaninsa da shugabannin unguwar.

    Daya daga cikin wadanda ke halartar taron ta shaida wa manema labarai cewa, mutumin ya shiga wajen ne a ranar Lahadi yana ihu yana cewa " Sai na kashe ku gaba daya" inda daga bisani kuma ya bude wuta da wata 'yar karamar bindiga.

    Biyu daga cikin wadanda suka samu raunin mata ne, sauran biyun kuma maza.

    Firaminista Giorgia Meloni, ta bayyana daya daga cikin matan da aka kashen Nicoletta Golisano, a matsayin kawarta, sauran matan da aka kashen kuma su ne Elisabetta Silenzi da kuma Sabina Sperandio.

  2. Shugabannin Afirka sun tafi taron Amurka da Afirka a Washington

    Shugabannin Afirka sun tafi Washington gabanin taron Amurka da kasashen Afirka da shugaba Biden zai dauki nauyi.

    Taron na yini uku za a fara ne daga ranar Talata, kuma zai mayar da hankali ne a kan kokarin da gwamnatin Biden ke yi ga kasashen Afirka.

    Shugabanni kasashen Afrika 49 da kuma shugaban hukumar tarayyar Afirka Moussa Faki Mhamat ne aka gayyata taron.

    Ba a gayyaci shugabannin kasashen Mali da Sudan da kuma Burkina Faso ba, saboda dakatar da su da kungiyar tarayyar Afirka ta yi, Eritrea ma ba za ta halarci taron ba.

    Tuni wasu daga cikin shugabannin da suka tafi taron suka wallafa batun tafiyar tasu a shafukansu na tiwita.

    Kauce wa X, 1
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X, 1

    Kauce wa X, 2
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X, 2

    Kauce wa X, 3
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X, 3

  3. Fitaccen mawakin Najeriya Wizkid ya nemi afuwa saboda rashin zuwansa Ghana wasa

    Wizkid
    Bayanan hoto, Wizkid

    Fitaccen mawakin Najeriyar nan Wizkid, ya nemi afuwa saboda rashin zuwansa wasa Ghana kamar yadda ya tsara.

    Wizkid, wanda sunansa na ainihi Ayodeji Ibrahim Balogun, ya kamata ya yi wasa a filin wasa na Accra a ranar Asabar.

    To amma bai samu damar zuwa ba abin da ya fusata 'yan kasar ciki har da wadanda suka shafe sa'oi a filin wasan suna jiran zuwansa.

    Wadanda suka shirya wasan sun zargi mawakin da saba alkawari.

    To amma a ranar Lahadi da daddare, mawakin ya nemi afuwar mutanen da suka shirya wasan dama wadanda suka shafe sa'oi suna jiran zuwansa, inda ya yi alkawarin samu ware wani lokaci a gaba don zuwa kasar ya yi wasa.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  4. An kama sojojin Chadi da dama bisa kitsa juyin mulki

    Deby

    Asalin hoton, Reuters

    Sojoji da dama ciki har da jami'an kabilar Zaghawa na shugaban kasar Chadi, Janar Mahamat Idris Deby aka kama a karshen mako bisa zargin kitsa juyin mulki.

    Rahotanni sun ce yanzu haka ana tsare da su zuwa lokacin da jami'an hukumar leken asirin kasar za su kammala bincike.

    Babu wata sanarwa a hukumance daga mahukunta a kan zargin kitsa juyin mulki, to amma bayanan hakan sun fito ne bayan da aka murkushe wasu 'yan adawa a wata gwabzawa da aka yi tsakanin jami'an sojin da kuma 'yan adawa a watan Oktoban da ya wuce.

    .

  5. Barkanmu da safiyar Litinin

    Masu bibiyar wannan shafin ni ce Aisha Shariff Baffa nake muku barka da safiyar Litinin - Mande tushen aiki, kamar yadda Hausawa kan ce.

    Ku kasance da ni tsawon wannan rana domin karanta labaran da suka shafi rayuwarku.

    Kuna iya tafka muhawara da bayyana ra'ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta a bbchausa.