Buhari ya ce yanzu Osinbajo ne ke da wuƙa da nama

Wannan shafi na kawo muku abubuwan da ke faruwa a sassan duniya kai-tsaye, musamman game da yaƙin Ukraine.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. Ƙarin 'yan Najeriya daga Ukraine 709 sun koma gida cikin dare

    Abuja

    Asalin hoton, Nidcom

    Ƙarin 'yan Najeriya 709 da suka maƙale sakamakon yaƙi a Ukraine sun sauka a Abuja a yau Lahadi daga Romania.

    Matafiyan akasarinsu ɗalibai sun sauka a filin jirgi na Nnamdi Azikwe da misalin ƙarfe 12:30 na dare a jirgin Airpeace.

    Wannan ne rukuni na uku da aka ɗebo daga ƙasashe maƙotan Ukraine da suka haɗa da Poland da Romania da Slovakia.

    Hukumar 'yan Najeriya mazauna ƙasashen waje ta ce nan gaba kaɗan wani jirgin zai sauka a Abujar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. 'Rasha na luguden wuta kan garuruwa don ta karya lagon 'yan Ukraine'

    Luguden wutar da Rasha ke yi a kan wuraren da farar hula ke zauna yunƙuri ne na karya gwiwar mazauna Ukraine, a cewar ma'aikatar tsaro ta Birtaniya.

    Cikin bayanan sirri da take bayarwa a kullum, ma'aikatar ta ce har yanzu jajircewar sojojin Ukraine na bai wa Rasha mamaki wadda daga baya ta fara kai wa garuruwan Kharkiv da Chernihiv da Mariupol hare-hare.

    Ta kwatanta ayyukan Rasha a Ukraine da waɗanda ta yi a Syria a 2016 da kuma yaƙin Chechnya a 1999, lokacin da Rasha ta ragargaza gine-gine.

    Rahoton ya ce harin da sojojin Ukraine ke kaiwa kan hanyoyin dako ya haddasa wa dakarun Rasha tsayawa cak ba tare da ci gaba da nausawa ba.

  3. Shugaban Turkiyya Erdogan zai tattauna da Putin

    Ukraine

    Asalin hoton, EPA

    A yau Lahadi ake sa ran Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan zai tattauna da Shugaba Vladimir Putin a kokarin da kasashen duniya ke yi na shawo kan yakin da ya kaddamar a Ukraine.

    Mai magana da yawun Mista Erdogan ya ce za su yi wa Rasha tayin zaman tattaunawar sulhu tsakaninsu da Ukraine da Turkiyya za ta karbi bakunci.

    A karon farko tun bayan barkewar rikicin, Mista Putin ya gana da firaministan Isra'ila Nafthali Bennett a fadar Kremlin.

    Wakilin BBC ya ce jami'an Isra'ila sun ce da safiyar nan ne Mr Bennett ya tafi birnin Moscow, kafin ganawa da Putin, sun kuma shafe sa'o'i 3 suna tattaunawa.

  4. Abubuwan da muka sani a kwana na 11 da fara yaƙi

    Ukraine

    Asalin hoton, Reuters

    Yayin da aka shiga kwana na 11 da fara kai hare-haren Rasha a Ukraine, mun samu rahotannin da ke cewa an ci gaba da jin ƙarar jiniyar da ke ankarar da mutane idan an kai hari a garin Poltava da ke tsakanin Kyiv babban birnin ƙasar da Kharkiv.

    Ga sauran abubuwan da ya kamata ku sani:

    • Shugaban Ukraine Zelensky ya sake kira ga ƙasashen Yamma su ayyana dokar hana zirga-zirgar jirage a Ukraine ɗin wato no-fly zone cikin wata tattaunawa da ya yi ta bidiyo da 'yan majalisar Amurka 300 a jiya Asabar. ya kuma tattauna da Shugaban Amurkar Joe Biden
    • Ƙawancen ratso na Nato ya ci gaba da yin watsi da buƙatar saka no-fly zone, suna masu cewa hakan zai saka su cikin rikici kai-tsaye da Rasha
    • Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi gargaɗin cewa zai ɗauki saka no-fly zone a matsayin yaƙi
    • Rashar na ci gaba ɓarin wuta a garin Mariupol da ke kudancin ƙasar. Yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma ta karye, wadda aka sa ran fararen hula za su fita daga garin
  5. Barka

    Za mu ci gaba da kawo muku yadda take kasancewa a fagen dagar da Rasha ta buɗe yayin da take ci gaba da kai hare-hare a Ukraine tun daga ranar Alhamis, 24 ga watan Fabarairu.

    Ku biyo ni Umar Mikail a wannan shafin don samun rahotannin kai-tsaye.