Za a rufe makarantu a Indiya saboda gurɓacewar iska

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar da ke tabbatar da kyau da ingancin iskar da ake shaƙa ta kasar Indiya, ta bayar da umarni ga kananan hukumomin birnin Delhi da makwabtan jihohi umarnin rufe makarantu saboda gurɓacewar iskar birnin.
Ba ya ga rufe makarantu har sai baba ta gani, hukumar ta kuma bayar da umarnin dakatar da duk wasu ayyuka na gine-gine da ba su zama na dole ba da kuma rufe tashoshin samar da makamashi a Delhi da makwabtan garuruwa har zuwa ranar Lahadi.
Haka kuma hukumar ta bukaci ofisoshin gwamnati da wadanda ba na gwamnati ba da su karfafa wa ma’aikatansu gwiwa kan su dinga aiki daga gida.
Sai dai wannan mataki na rufe wurare tare da takaita yawan jama’a a waje bai yi wa wasu talakawa dadi ba, wadanda suka samu kansu a yanayi na gaba kura baya sayki.
"Ba shakka akwai matsala," a cear wani makanike. "Rashin numfashi da kaikayin ido ne suka fi illa. Ta yaya za mu iya tsira daga wannan? Dole ne mu zauna a gida domin guje wa gurbatar iskar. "Amma idan muka kuma zauna a gida ta yaya za mu rayu?’’

