Magoya bayan Trump sun tayar da rikici a Majalisar Dokokin Amurka

Wannan shafi ne da ke kawo muku abarai da rahotanni na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sasssan duniya a ranar da muka shiga sabuwar shekarar 2021.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Halima Umar Saleh

  1. Ba za a tuhumi ɗan sandan da ake zargi da kashe Jacob Blake ba

    Masu gabatar da ƙara a jihar Wisconsin da ke Amurka sun ce ba za a tuhumi ɗan sanda farar fatar nan da ake bincika kan harbin baƙar fata Jacob Blake ba, wanda aka kashe a birnin Kenosha cikin watan Agusta.

    Mista Blake ya samu shanyewar jiki sanadiyyar lamarin da ya janyo rikici sosai.

    Lauyan Blake ya bayyana rashin jin daɗinsa game da hukuncin, inda ya ce akwai isassun hujjoji da suka isa su sa a tuhumi ɗan sandan.

    Masu gabatar da ƙara sun ce Mista Blake yana riƙe da wuƙa a lokacin arangama da ɗan sanda kuma jami'in Rusten Sheskey zai yi iƙirarin cewa ya harbe shi ne don kare kansa.

    Wani bidiyo da ya ɓulla a shafukan zumunta ya nuna yadda ɗan sandan ya harbi Blake a baya sau bakwai yayin da yake komawa cikin motarsa bayan 'yan sandan sun tsayar da shi.

  2. An kama matashi da zargin kashewa tare da ƙone gawar wani a Bauchi

    Bayanan sautiLatsa hoton sama ku saurari rahoton Abdussalam Ibrahim Ahmed

    'Yan sandan Jihar Bauchi sun ce suna neman wani malami ruwa a jallo da take zargi da hannu wurin kashe wani matashi tare da ƙwaƙule masa ido.

    Kakakin 'yan sandan jihar ya shaida wa BBC cewa tuni suka kama wani matashi ɗan shekara 17 mai suna Musa Hamza bayan ya kashe mutumin kuma ya ƙwaƙule idanunsa sannan ya ƙona gawar tare da binne ta a garin Alƙaaleri.

    Musa ya bayyana cewa malamin ne ya umarce shi da yin hakan domin ya kawo a haɗa masa layar ɓata.

    Wannan na zuwa ne ƙasa da mako guda bayan an kama wani matashi da zargin yanke wa wata yarinya 'yar shekara shida al'aurarta a garin Jama'are na Jihar ta Bauchi.

    Yanzu haka dai hukumar ta ce ta baza komar neman malamin da kuma wani matashi da aka haɗa baki da shi wurin yanke yarinyar.

  3. Jam'iyyar Biden na dab da samun rinjaye a Majalisar Dattawan Amurka

    Joe Biden

    Jam'iyyar Domocrat ta zaɓaɓɓen Shugaban Amurka Joe Biden na dab da karɓe jagorancin Majalisar Dattawan ƙasar yayin da sakamakon zaɓen sanata biyu daga Jihar Georgia ke fitowa.

    An hasaso cewa Raphael Warnock, wani fasto daga Atlanta, shi ne zai lashe kujerar sanata ɗaya, yayin da ɗayar take reto tsakanin Democrat da Republican a yanzu.

    Idan Democrat ta ci duka biyun, Mista Biden zai fi samun damar aiwatar da manufofinsa a majalisun ƙasar.

    Ana aiwatar da zaɓen ne a zagaye na biyu saboda dokar Georgia, wadda ta ce lallai ne sai ɗan takara ya samu kashi 50 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa kafin ya ci zaɓe.

    Babu ɗan takarar da ya samu kashi 50 a babban zaɓen da aka yi a watan Nuwamban 2020.

  4. Jihar Kwara ta lashe kyautar naira biliyan shida daga Bankin Duniya

    Gwamnan Kwara

    Asalin hoton, @followKWSG

    Bayanan hoto, Gwamnan Jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq

    Gwamnatin Jihar Kwara a Najeriya ta yi nasarar lashe kyautar dala miliyan 16.9 daga wani shirin Bankin Duniya na shekarar 2019/2020 mai suna State Fiscal Transparency, Accountability and Sustainability (SFTAS) da ke sa ido kan kasafi da kashe kuɗaɗen gwamnati.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kyautar ita ce mafi girma da jihar ta taɓa lashewa tun bayan fara aiwatar da ita a 2018, inda kuɗin suka kai kusan naira biliyan shida da rabi.

    Mai magana da yawun Ma'aikatar Kuɗi da Tsare-Tsare ta Jihar Kwara, Saad Hamdalat, ita ce ta sanar da samun kyautar cikin wata sanarwa da fitar a jiya Talata, kamar yadda jairdar ta wallafa.

    Ta ce sun yi nasarar ce sakamakon cimma buƙatun da aka sharɗanta a kundin duba ayyuka da jami'an tantancewa suka miƙa bayan sun ziyarci jihar.

    "Sharuɗɗan sun ƙunshi kyautata yadda ake bayar da rahoto kan kasafin kuɗi da saka 'yan ƙasa a cikin tsare-tsaren kasafin da nemo ƙarin hanyoyin tattara kuɗin haraji na cikin gida da kuma yin amfani da shaidar yatsa da lambar banki ta BVN don daƙile zamba wurin biyan albashi," in ji ta.

    Game da kuɗin kuwa, ta ce tuni jihar ta karɓi dala miliyan 9.4 ranar 4 ga Janairun 2021 kuma tana jiran miliyan 2.5 nan gaba a watan, bayan ta karɓi miliyan biyar a Nuwamban 2020.

  5. Ƙasashen Turai sun fi tallafa mana fiye da na Musulmai - Gwamna Zulum

    Gwamnan Jihar Borno Babagana Umara Zulum

    Asalin hoton, @GovBorno

    Gwamnan Jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce ƙasashen Turawa sun fi taimaka wa jiharsa fiye da Larabawa Musulmi yayin da suke fama da hare-haren ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

    Zulum ya bayyana hakan ne a jiya Talata yayin da yake karɓar baƙuncin jakadan Falasɗinawa Saleh Fheied Saleh a Maiduguri, babban birnin jihar.

    "Ni mutum mai aiki da zahiri, tun bayan da muka shiga cikin matsalolin nan, mun samu tallafi daga Birtaniya da sauran sassan Turai da Amurka da Canada da Japan da sauran waɗanda suka nuna damuwarsu garemu," in ji gwamnan.

    "Sai dai irin wannan tallafi bai taɓa zuwa daga ƙasashen Larabawa ba, waɗanda muke addini ɗaya (Musulunci) da kuma al'ada. Har Shuwa Arab muna da su a Borno, abin da ke nuna yadda tarihinmu ke da alaƙa.

    "Mun yi yunƙuri iri-iri, mun je ofisoshin jakadancin ƙasashen Larabawa musamman masu arziki, amma da yawan ƙasashen Larabawa ba su damu da halin da muke ciki ba kuma ba su ba mu taimako ba."

    Gwamna Zulum ya kuma bayyana ziyarar jakadan da cewa mai "ƙarfafa gwiwa" kuma ya gode masa.

    A nasa ɓangaren, Ambasada Saleh Fheied ya bayyana cewa akwai 'yan asalin Jihar Borno a Falasɗin, ciki har da wata mai suna Fatima Barnawi da ta taɓa zama minista kuma babbar jami'ar 'yar sanda.

    "Akwai kamfanonin Falasɗinu da yawa a Najeriya da suke son yin aiki tare da gwamnatin Borno kuma za mu yi duk abin da kuke buƙatar mu yi domin taimakawa," in ji jakadan.

    Rikicin Boko Haram ya yi sanadiyyar kashe mutum fiye da 36,000 a jihohin arewa maso gabashin Najeriya tare da jawo asarar dukiya mai ɗumbin yawa cikin shekara fiye da 10.

  6. Kim Jong-un ya yarda ƙasarsa na cikin matsalar tattalin arziki

    Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong-un ya tabbatar da ƙalubalen da tattalin arzikin ƙasarsa ke ciki a wani jawabin buɗe babban taron jam'iyyarsa ta Workers Partymai mulkin ƙasar.

    Mista Kim ya ce shirin shekara biyar na baya-bayan nan da aka yi ya gaza matuƙa wurin biyan muradun jam'iyyar, inda ya ce akwai ƙalubale na ciki da waje da ke yi wa ci gaban ƙasar ƙafar ungulu.

    Ya bayyana cewa zai ci gaba da gwagwarmaya domin ganin haɗin kan Koriya da inganta alaƙa da ƙasashen waje.

  7. Najeriya da ƙasashen OPEC za su ƙara yawan man da suke fitarwa

    Haƙo man fetur

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur, wadda Najeriya ke ciki, ta Organisation of Petroleum Exporting Countries (OPEC) da wasu da ba 'yan ƙungiyar ba sun amince su ƙara yawan man da suke haƙowa da ganga 500,000 kowace rana a watan Janairu.

    Ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne yayin taronta karo na 13 tsakanin 'yan OPEC da kuma ministocin ƙasashen da ba sa cikinta mai suna ONOMM, wanda aka yi a birnin Vienna na Austria jiya Talata.

    Taron ya aminta cewa a koma fitar da ganga miliyan biyu a kowace rana zuwa kasuwa, amm za a bar kasuwa ta fayyace sanda za a kai ga yawan adadin hakan.

    Za a fayyace abin da ya kamata a fitar a watannin Fabarairu da Maris nan gaba kaɗan.

    Daga watan Mayu zuwa Nuwamba, ƙasashen masu arzikin fetur sun amince su rage man da suke fitarwa zuwa kasuwar duniya da kusan ganga biliyan 1.9, abin da ya taimaka wurin farfaɗo da darajar man a kasuwar duniya.

    Farashin man fetur ya yi mummunar faɗuwa a 2020 sakamakon annobar korona, wadda ta hana hada-hadar kasuwanci a faɗin duniya.

  8. Cutar korona a Najeriya: Mutum ɗaya ya mutu, 1,354 sun kamu ranar Talata

    Cutar korona

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 1,354 da suka kamu da annobar korona ranar Talata.

    A cewar bayanin da NCDC ta wallafa a shafinta na Tuwita, cikin sa'a 24 da ta gabata, mutum ɗaya ne cutar ta yi ajalinsa sannan mutum 697 sun warke kuma an sallame su daga asibiti.

    Har yanzu jihar Legas ce ke da kashi mafi tsoka na mutanen da suka kamu da cutar cikin kwana ɗaya inda take da mutum 712 sai Abuja, babban birnin ƙasar mai biye mata da mutum 145.

    Jihar Plateau ce ta uku da mutum 117 yayin da a Kwara aka samu ƙarin mutum 81 sai Kaduna mai mutum 54 inda a Sokoto kuma aka samu mutum 39.

    Oyo na da mutum 38, Rivers 37, Gombe 21, Enugu 20, Akwa Ibom 16 sai Bauchi da Delta da aka samu mutum 14 a kowace jiha.

    A Ebonyi kuma mutum 13 ne suka harbu ranar Talata inda Anambra ta rawaito mutum 9 sun kamu da cutar cikin kwana ɗaya.

    Taraba da Edo, an samu mutum 8 kowace jiha da suka kamu da cutar sai jihar Kano mai mutum 3, Osun 2, Ekiti ma tana da mutum biyu inda a Ogun aka samu mutum ɗaya da ya kamu da korona ranar Talata.

    Da wannan ƙididdiga, adadin mutanen da suka harbu da cutar korona a Najeriya sun kai 92,705 sannan an sallami mutum 76,396 daga asibiti bayan an tabbatar sun warke daga cutar kuma mutum 1319 ne suka mutu tun bayan ɓullar cutar a ƙasar.

  9. Barkanmu da hantsin Laraba - ta bawa ranar samu

    Ku biyo ni Umar Mikail domin samun labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a sassan duniya.

    Sai dai za mu fi mayar da hankali kan Nijar da Najeriya da maƙwabtansu.