Korona a Najeriya: Mutum uku sun mutu, 501 sun kamu ranar Lahadi

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 501da suka kamu da cutar korona a ranar Lahadi.
Kazalika, ƙarin wasu mutum uku sun mutu sakamakon cutar.
Jihar Legas ce ke da adadi mafi yawa da mutun 218, yayin da Abuja ke bi mata da mutum 112.
Koronar ta kuma kama mutum 53 a Kaduna, sai Plateau mai mutum 24, sai Katsina mai 21.
Jihar Kano na da 16 sai kuma Yobe mai mutum 14. A Ondo an samu mutum 10 sai Ogun 9, Edo 7, Bayelsa 5.
Jihohin Rivers da Borno na da 4-4, yayin da Osun da Ekiti suka rufe jadawalin da mutum 2-2 kowannensu.
A jimillance adadin mutunen da cutar ta kama tun daga bullarta zuwa yanzu sun kai 78,434, yayin da 68,303 suka warke aka kuma samu asarar rayuka 1,221.
