Fursunoni 200 sun tsere daga gidan yari

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umaymah Sani Abdulmumin and Nasidi Adamu Yahaya

  1. Tanzania ta dage haramcin da ta ƙaƙaba wa jiragen saman Kenya

    Tanzania ta ɗage haramci da ta ƙaƙaba wa kamfanonin jiragen saman Kenya.

    Sanarwar da ma'aikatar sufurin jiragen saman Tanzania ta fitar, ta ce ta ɗage haramcin kuma nan take ta amince jiragen su ci gaba da hada-hada tsakanin ƙasashen biyu.

    Matakin na zuwa ne kwana guda bayan Kenya ta ware Tanzania cikin ƙasashen ƙetare da za su killace kansu na kwana 14 saboda annobar korona idan sun shiga ƙasar ta.

    Tanzania yanzu ta shiga sawun ƙasashen 146 da ƴan ƙasar za su iya shiga Kenya ba tare da killace kai ba.

  2. Baban mai kuɗin duniya ya rasu

    William Gates

    Asalin hoton, BillGates

    Mahaifin Bill Gates, ɗaya daga cikin attajiran duniya wanda ya samar da kamfanin Microsoft ya mutu.

    William Henry Gates II ya mutu a ranar Litinin ya na da shekara 94.

    Cutar Alzheimer da ke shafar ƙwaƙalwa ce ta yi sanadi mutuwarsa, kamar yadda iyalansa suka tabbatar a wani labarin da jaridar New York ta wallafa.

    Gates Babba tsohon soja ne kuma ya kafa kamfani da ke harkokin shari'a, kamar yadda tarihinsa ya nuna.

    Bill Gates mai shekara 64, ya ce sun yi babban rashi kuma zai dauke su tsowon lokaci su na jimamin mutuwar mutumin da ya yi tasiri a rayuwar mutane da dama.

  3. ‘Yan sanda ba abokanmu ba ne, in ji Ƴan Twitter

    SARS

    Asalin hoton, SARS

    Mabiya shafukan sada zumunta na Tuwita a Najeriya sun yi wa ƴan sandan ƙasar ca, musamman ma na rundunar nan ta musamman mai yaƙi da fashi da makami da ake kira SARS.

    Hakan ya biyo bayan mutuwar wani matashi ne da ake zargin ƴan sandan ne sanadi wanda suke zargin sa da kasancewa ''ɗan damfara'' da aka fi sani da ''Yahoo Boys'' a Osogbo, babban birnin Jihar Osun.

    Rahotanni sun ce ƴan sanda sun bi matashin tare da wasu matasan uku a mota, inda a ƙoƙarinsu na tsere wa ƴan sandan suka yi hatsarin da ya yi sanadin mutuwar yaron a ranar Talata da yamma.

    Matashin mai suna Remi a take yanke ya mutu, yayin da aka garzaya da sauran ukun da suka jikkata asibiti.

    Tuni dai mazauna birnin suka ce matasa sun fara zanga-zangar nuna taƙaicinsu kan lamarin.

  4. Ƴan siyasar Najeriya za su fuskanci haramcin bisar shiga Burtaniya

    Boris Johnson

    Asalin hoton, Getty Images

    Burtaniya ta yi barazanar sanya haramci kan duk wani ɗan Najeriya da aka samu da hannu a rikicin zaɓe, gabanin zaɓukan gwamnan da ke tafe a Najeriya a karshen wata.

    Sannan ta yi barazanar datse kadarorin ketare na duk wani ɗan siyasa da aka samu da laifi.

    A sanarwar da ta fitar, Burtaniya ta ce za ta tura masu sa ido a zaɓukan gwamnan jihohin Edo da Ondo.

    Jakadan Burtaniya a Najeriya ya tattauna da shugabannin manyan siyasar ƙasar biyu domin jan hankalinsu da bukatar zaɓe cikin kwanciyar hankali.

    A ranar 19 ga watan Satumba za a gudanar da zaɓen Edo, sannan 10 ga watan Oktoba na Ondo.

    Masu sa ido daga ƙetare sun zargi ƴan siyasar Najeriya da amfani da salon rikici da tsangwama a zabukan baya.

    A ranar litinin ƙasar Amurka ta sanya haramcin bisa kan wasu ƴan siyasar ƙasar da take zargi da yiwa demokradiya zagon-kasa gabanin zaben da ke tafe.

    Zabe

    Asalin hoton, Getty Images

  5. Ruftawar gini ta kashe ƴan gida daya a Kano

    Kano

    Asalin hoton, Daily Trust

    Wani gini mai hawa ɗaya ya rufta tare da iyalai ƴan gida ɗaya a Kano, mutum biyu sun mutu.

    Rahotannin sun ce ginin ya rufta ne tare da mutum 10, sannan jami'an agaji sun yi ƙoƙarin ceto mutum 8 da suka maƙale a cikin ɓaraguzai.

    Lamarin ya faru ne a yankin Gwammaja Ƴan kosai da ke ƙaramar hukumar Dala ta jihar Kano.

    Kakakin hukumar kashe gobara, Malam Sa'idu Muhammed, da ke tabbatar da faruwar lamarin ya ce ginin ya rufta ne a cikin dare ana tsaka da tafka ruwa kamar da bakin-ƙwarya.

    Wadanda suka mutu yara ne ƴan shekara 4 da 6.

    Gwammaja
  6. Shin za ku iya tura wa mawaƙi kudi don waƙe ɗan siyasa?

    A makon da ya gabata ne fitaccen mawaƙin siyasar nan Dauda Kahutu Rarara ya ce sai an biya shi kudi zai yi wa shugaba Buhari waƙa.

    Kwanaki kaɗan da faɗar hakan sai ga wasu mawaƙan kamar Adam A Zango da Abubakar Sani sun ce su ma a tara musu kuɗi domin yi wa gwananyen su waƙa.

    Maganganun nasu dai sun jawo tayar da jijiyar wuya daga ƴan ƙasa inda wasu suka dinga sukar su wasu kuma na goyon bayan aniyar tasu.

    A wannan bidiyon BBC ta yi wani nazari ne kan wannan batu.

    Bayanan bidiyo, Shin za ku iya turawa dan mawaki kudi don wake dan siyasa?
  7. Majalisar Japan ta aminta da nadin Yoshihide Suga a matsayin sabon firanminista

    Yan majalisa a Japan sun aminta da a naɗa Yoshihide Suga a matsayin sabon firaiminista.

    Hakan ya biyo bayan kasancewar sa sabon shugaban jam'iyyar Liberal Democratic Party mai mulki.

    Firaiminista mai ci, Shinzo Abe ya bayyana cewa zai yi murabus saboda ba shi da isashen lafiya.

    Ana saran Mr Suga zai gaji matsalar tattalin arziki da annobar Korona da kuma rikicin siyasa da China.

  8. Amurka ta ƙaƙaba takunkumi kan matar tsohon shugaba Jammeh na Gambia

    Gambia Jammeh

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar tsaron Amurka ta sanar da ƙaƙaba takunkumin karayar tattalin arziki kan Zineb Jimmeh, matar tsohon shugaban Gambia, Yahya Jammeh.

    Ana ganin Zinab ta taka muhimmiyar rawa da taimaka wa mijinta wajen aikata rashawa a tsawon shekaru 22 da suka kwashe suna mulki a kasar ta yammacin Afirka, a cewar sanarwar ma'aikatar.

    "Zineb Jammeh ta bada gudunmawa da taimakawa mijinta. Ta taimakawa mijinta ta hanyar amfani da sunan gudauniya da kungiyoyin agaji wajen wawushe dukiya da halasta kudi ta haramtacciyar hanya," a cewar sanarwar.

    Tsohon shugaban ya mulki Gambia sama da shekara 20. Ya tsere daga ƙasar bayan rashin nasara a zaben 2017 inda yanzu haka yake mafaka a Equatorial Guinea.

  9. Juyin mulki a Mali: An tashi baram-baram kan batun kafa gwamnatin riƙo

    An kammala taro tsakanin Sojoji da sauran masu ruwa da tsaki kan batun mai da mulki hannun farar hula ya kare ba tare da an cimma matsaya ba.

    Hakan na nufin sojojin sun wuce wa'adin da ƙungiyar ECOWAS ta basu na su bayyana matsayar su kan batun.

    Masu ruwa da tsakin sun tattauna batun tsawon lokacin da gwamnatin rikon ƙwarya kashe a kan mulki, da kuma takunkumin da a ka kakaba wa Malin.

    Shugabanni daga ƙasashe takwas na yammacin Afirka, da wakilan majalisar dinkin duniya da na ƙungiyar tarayyar Afirka ne suka gudanar da taron a birnin Accra na ƙasar Ghana a jiya Talata. Da nufin kwakkwafe shawara, kan batun shirin mayar da kasar Mali kan turban mulkin dimokuradiyya.

    Latsa nan don karanta karin bayyani

  10. Budewa

    Masu bibiyar mu a wannan shafin muna muku marhaba da fatan an wayi gari lafiya. Umaymah Sani Abdulmumin ke fatan kasancewa da ku, za mu rinka duba da kawo muku abubuwan da ke faruwa kai tsaye a Najeriya da Nijar da ma sauran sassan duniya.