Gwamnati ta gargadi 'yan Najeriya kan cutar Coronavirus

Wannan shafi yana kawo maku irin wainar da ake toyawa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da Ghana da sauran kasashen Afirka da ma fadin duniya.

Rahoto kai-tsaye

  1. Koriya Ta Kudu

    Korea Koriya ta Kudu za ta aike da jirgin soji tekun Hormuz don taimaka bai wa safarar jiragen ruwa na dakon kaya damar wucewa.

    Wannan mataki dai Amurka ce ta bukaci Koriya ta Kudun ta taimaka don gadin jiragen dakon mai, a daidai lokacin da dangantaka tsakaninta da Iran ke kara lalacewa.

    Ma'aikatar tsaron Koriyan ta tabbatar da cewa tawagar ta za su aiki na daban, ba irin wanda kawancen Amurka ke jaoranta ba.

    Tun a shekarar 2009 ne Koriya ta Kudu ta girke jirgin soji da ke yaki da masu fashin teku a tekun Aden da ke arewacin Yemen, ta dayan bangaren kuma a gabashin Afirka.

    Kwamandojinta sun yi fice wajen yaki da 'yan fashin teku, musamman fafatawarsu da 'yan fashin Somaliya a shekarar 2011 a lokacin da suka kubutar da tankokin kasarsu.

  2. Babban limamin Ghana ya shiga sahun Musulmi 500 masu fada-a-ji na duniya

    sharubutu

    Asalin hoton, AFP

    Limamin limamai na Ghana, Dr Sheikh Osmanu Nuhu Sharubutu, da kuma jagoran kungiyar agaji ta Islamic Council for Development and Humanitarian Services (ICODEHS), sun shiga sahun musulmi 500 masu fada-a-ji a duniya na shekarar 2020.

    Cibiyar binciken Musulunci ta Royal Islamic Strategic Studies Center ta kasar Jordan, wadda ta shirya wannan karramawa, ta yi karin bayanin cewa an karrama wadannan mutane ne saboda irin ayyukan agaji da jin kai da suke yi a cikin Ghana da ma yammacin Afrika.

    Wakilinmu a Ghana Muhammad Fahd Adam ya aiko mana da Karin bayani a cikin rahotonsa daga Accra.

    Bayanan sautiRahoton Fahd kan girmama limamin limamn Ghana Sharubutu
  3. 'Dakarun tsaron Kamaru sun kashe mutum 75 a mako guda'

    Ana zargin dakarun tsaron gwamnatin Kamaru da kisan araren hula 75 tare da kona kusan gidaje 600 a cikin mako guda a Yankin Renon Ingila.

    Wakilinmu da ke Kamaru Mohamman Babalala ya ruwaito cewa wannan lamarin ya faru ne a lokacin da hukumomi suka ce sun aika daruruwan dakarun tsaro yankin domin su karfafa tsaro a lokacin zaben da zai gudana nan da makwanni uku.

    Sai dai kakakin Ma’aikatar Tsaro ya musanta duk wadannan zarge-zargen.

    Lamarin ya faru ne a lokacin da hukumomi suka ce sun aika daruruwan dakarun tsaro yankin

    Asalin hoton, Getty Images

  4. Mexico: Ana kokarin hana 'yan ci-rani shiga Amurka

    Hukumomi a Mexico sun yi kokarin hana daruruwan 'yan ci-rani daga tsakiyar Amurka tsallake kogin da ya raba kasar da Guatemala a kokarin su na shiga Amurka.

    Jami'an tsaron Mexico cikin damara sun yi nasarar kama wasu daga cikin wadanda suka tsallaka kogin, duk da cewa 'yan ci-ranin sun yi ta jifan su da duwatsu.

    Wakilin BBC ya ce duk da kiran da 'yan ci-ranin suka yi wa 'yan sanda, tare da cewa suna son ketarawa don samun ingantacciyar rayuwa a Amurka.

    Hukumomin Mexico sun hana su ci gaba da balaguron.

    A bangare guda, Mexicon ta yi musu tayin ayyukan yi, idan suka amince su zauna a kudancin kasar, tare da hana su shiga Amurka.

    'Yan ciranin Mexico

    Asalin hoton, AFP

  5. China na son dakile yaduwar cuta mai alaka da numfashi

    Kasar China na fadi tashin dakile yaduwar cuta mai alaka da nunfashi da ta bulla a kasar, bayan jami'an lafiya sun ba da tabbacin ana iya yada ta daga wani zuwa wani.

    Ana tantance fasinjoji a tashoshin jiragen kasa da sama, a daidai lokacin da dubban 'yan kasar ke balaguron zuwa bikin sabuwar shekara.

    Farfesa Jennifer Nuzzo kwararriyar likita ce a cibiyar hana yaduwar cutaka ta Amurka, ta ce ''ba mu san yadda cutar ke yaduwa tsakani mutane cikin sauri, ba kamar yadda muka gani a lokacin da cutar SARS da MARS suka bulla shekarra 2003 ba.'

    ''Mun damu matuka kan yadda cutar ke kara yaduwa ba ga wadanda sukai mu'amala da juna kadai ba, saurin yaduwar yana ba mu tsoro.''

  6. Mutum miliyan 500 ke yin ayyukan da ba sa muradi a duniya

    rashin aikin yi

    Asalin hoton, Getty Images

    Sabuwar kididdigar da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, ta nuna kusan mutum miliyan 500 ne ke yin ayyukan da ba sa muradi, ko ma ba sa so sam.

    Hukumar Kwadago Ta Duniya ta ce rashin aikin yi ga al'umma zai karu da miliyan 2,500,00 a wannan shekara, sakamakon tattalin arzikin duniya da ya kasa tsayawa da kafafunsa.

    Hukumomin sun yi amanna wannan abin damuwa da dubawa ne, a daidai lokacin da takardun neman aiki suka cika masana'antu da ma'aikatu da sauran wurare.

    Hukumar kwadagon ta ce matsalar rashin daidaito tsakanin maza da mata a wuraren ayyuka, da ratar shekaru, da ainahin inda ayyukan suke duk abin damuwa ne.

    An kuma samu karuwar zanga-zanga, da yajin aikin a kasashen duniya tsakanin shekarun 2009 da 2019.

  7. Labaran ranar Talata 21 ga watan Janairun 2020

    Masu bin mu a wannan shafi assalamu alaikum. Barkanmu da safiya.

    Sai ku biyo mu a wannan shafi don karanta labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da sauran sassan duniya a yau Talata.

    Kuna iya duba kasa don karanta labaran abubuwan da suka faru a jiya Litinin.

    Halima Umar Saleh da Nabila Mukhtar Uba ne za su jagoranci kawo labaran a wannan safiya, kafin daga bisani su mika ragamar ga Usman Minjibir da Mustapha Kaita.

  8. Ban kwana

    Jama'a nan muka kawo karshen rahotannin kai-tsaye na abubuwan da suka faru a Najeriya da makwabta da ma sassan duniya.

    Da fatan za mu sake haduwa gobe da safe.

    Amma kafin nan, ku duba kasa domin karanta labaran yau Litinin.

  9. Gwamna Yahya Bello ya taya Gwamna Lalong murna

    Gwamnan jihar Kogi Yahya Bello ya taya gwamnan jihar Filato Simon Lalong murnar samun nasaara a shari'ar da Kotun Koli ta gudanar a yau Litinin a Abujan Najeriya.

    Kotun ta tabbatar da hukuncin da kotuna biyu suka yi ne a baya - ta sauraron kararrakin zabe da kuma ta daukaka kara, inda ta tabbatar da cewa gwamna Lalong ne ya lashe zaben na watan Maris din 2019.

    Simon Lalong

    Asalin hoton, Simon Lalong

    Bayanan hoto, Simon Lalong
  10. Rudiger ya bai wa kasar Saliyo tallafin kudi

    Antonio Rudiger

    Asalin hoton, Sierra Leon State House

    Dan wasan bayan kungiyar Chelsea kuma dan kasar Jamus, Antonio Rudiger ya ce kasar Saliyo "gida ce a wurina" yayin da yake bayar da taimakon kudi ga wata kungiya mai fafutikar samar da ingataccen ilimi kyauta a kasar mai suna Free Quality Education initiative.

    Mahaifan Rudiger 'yan asalin Saliyo ne da ke yankin Afirka ta Yamma amma an haife shi ne a Jamus kuma ya buga wa Jamus din wasa har sau 30.

    Dan shekara 26 din ya bai wa shugaban Saliyo Julius Maada Bio taimakon dala 101,000 a wurin taron zuba jari a Afirka da ke gudana a birnin Landan, wanda kuma Shugaba Buhari yake halarta.

    "Saliyo gida ce a wurina. Ba na cikin masu surutu ne kawai, na fi yin abu a aikace," Rudiger ya fada wa shugaban kasar yayin da yake mika taimakon.

    "Na shirya tsaf domin na sauya kasar Saliyo kuma kar ku ji ko dar wurin tambaya ta taimako kan ilimi," in ji Rudiger.

  11. Abin da gwamnonin da suka yi nasara ke fada

    Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya ce ba zai nuna wa kowa bambanci ba a jihar tasa biyo bayan tabbatar masa da kujerar gwamna da Kotun Koli ta yi a yau Talata.

    Kazalika gwamna Simon Lalong na jihar Filato ya roki 'yan hamayya na jam'iyyar PDP da su hada hannu da gwamnati domin ciyar da jihar tasu gaba.

    Tun da farko gwamnan kano ne Abdullahi Umar ganduje ya yi kira da 'yan jam'iyyar PDP a Kano da su mara wa gwamnati baya bayan hukuncin na Kotun Koli da ya kori karar Abba Gida-Gida.

    Abdullahi Ganduje

    Asalin hoton, KNSG

    Bayanan hoto, Abdullahi Umar Ganduje
    Simon Lalong

    Asalin hoton, Simon Lalong

    Bayanan hoto, Simon Lalong
    Bala Muhammad

    Asalin hoton, Bala Muhammad

    Bayanan hoto, Bala Muhammad
  12. Mutum 10 sun mutu a wurin bikin addini a Habasha

    'Yan kallo bikin addini a kasar Habasha

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Benen ya rufta da 'yan kallo ne ana tsaka da biki

    Akalla mutum 10 ne suka mutu a wurin wani bikin addini sannan sama da 100 suka jikkata bayan wani bene na katako da 'yan kallo ke kai ya rushe a garin Gondar na kasar Habasha wato Ethipia, a cewar rahoton AFP.

    "Ina shaida maku cewa zuwa yanzu gawar mutum 10 muka samu. Wadanda suka rasu kuma sun kai 100 ko ma 150," in ji wani likita a asibitin Jami'ar Gondar.

    Bikin na kwana biyu wanda aka fi sani da Timket a harshen Amharic, ana tunawa da baftisimar da aka yi wa Yesu Almasihu a Kogin Jordan.

    Garin Gondar wuri ne mai tarihi wanda fadar gwamnatin Ethiopia ta taba zama a ciki, ana yi masa kallon cibiyar bikin, inda tikitin jirgin sama zuwa garin ke karewa da wuri saboda rubibin zuwa.

    Ga wasu hotuna da aka dauka na bikin gabanin tsautsayin:

    Masu bikin Timket a Ethiopia
    Masu bikin Timket a Ethiopia
    Masu bikin Timket a Ethiopia
  13. Murnar nasarar Bala Muhammad

    Bauchi
    Bauchi
    Bauchi

    Mutane da dama ne suka yi ta nuna murnarsu a harabar kotun kolin Najeriya da ke birnin Abuja dangane da nasarar da ta tabbatar wa Gwamna Bala Muhammad.

  14. Kotu ta tabbatar da Bala Muhammad ta yi watsi da karar M. A Abubakar

    Bala Muhammad

    Asalin hoton, Bala Muhammad Twitter

    Dukkanin alkalan kotun ta Koli guda bakwai sun amince da korar karar tsohon gwamnan jihar Bauchi, M.A. Aubakar wanda yake kalaubalantar nasarar da Gwamna Bala Muhammad ya samu.

    Yayin zagaye na biyu na zaben da aka yi ranar 26 ga watan Maris din 2019, hukumar zabe jihar Bauchi ta tabbatar da cewa Bala Muhammad ya doke gwamna mai ci Muhammed Abdullahi Abubakar dan takarar jam'iyyar APC.

    PDP ta lashe zaben ne da kuri'a 515,113, yayin da APC da ke mulki a jihar ta samu kuri'a 500,625

    Sakamakon karamar hukumar Tafawa Balewa ne kadai dama ya rage, kuma PDP ce ta lashe karamar hukumar inda ta samu kuri'a 39,225, yayin da APC ta samu kuri'a 30,055.

    An ta kai komo zuwa kotu bisa sakamakon karamar hukumar Tafawa Balewa musamman tsakanin hukumar INEC da kuma jam'iyyar APC a jihar ta Bauchi, bayan da jam'iyyar ta kai hukumar kotu inda ta bukaci a dakatar da tattara sakamakon Tafawa Balewa.

  15. Najeriya za ta taimaka wa kasar Guinea gina matatar man fetur

    Simbi Wabote

    Asalin hoton, @officialncdmb

    Bayanan hoto, Simbi Wabote (na farko daga hagu) ne babban sakataren hukumar NCDMB

    Hukumar Kula da Ci Gaba da Sa Ido wato Nigerian Content Development and Monitoring Board (NCDMB) ta ce za ta hada kai da kamfanin Waltersmith Petroleum Oil Limited domin taimaka wa kasar Equatorial Guinea wurin gina kananan matatun man fetur.

    Babban sakatare a ma'aikatar, Mista Simbi Wabote ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da majalisar gudanarwar hukumar ta fitar a Abuja ranar Lahadi, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito.

    Sanarwar ta ce ya yi maganar ne a lokacin da ya karbi bakuncin ministan ma'adanai na Equatorial Guinea, Mista Gabriel Lima a harabar karamar matatar fetur mai tace ganga 5,000 a kullum da ake ginawa a Ibigwe na jihar Imo.

    Ya kara da cewa gina matatun na Equatorial Guinea zai bai wa Najeriya damar fitar da nata man sannan ta kara yawan ma'adanan da ake samarwa daga hydrocarbon.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  16. Kotun koli ta tabbatar wa Simon Lalong nasara ta yi watsi da karar Jeremiah Useni

    Gwamna Simon Lalong

    Asalin hoton, PSG

    Alkalan kotun koli sun kori karar dan takarar gwamnan jam'iyyar PDP na jihar Plateau, Jeremiah Useni, inda kotu ta tabbatar da Simon Lalong na jam'iyyar APC a matsayin mutumin da ya lashe zaben 2019.

    Sakamakon zaben zagaye na biyu da aka yi a ranar 26 ga watan Maris din 2019 ya nuna Gwamna Lalong ya kada tsohon ministan Abuja Jeremiah Useni na jam'iyyar PDP.

    An gudanar da zaben ne a mazabun kananan hukumomi tara wadanda ba a kammala ba a zaben farko na gwamna da aka gudanar a ranar 9 ga Maris.

    Jam'iyyar APC ta lashe kananan hukumomi guda shida a mazabun da aka sake zaben. Jam'iyyar PDP kuma ta lashe kananan hukumomi uku.

    Yanzu APC ta lashe kananan hukumomi 11 cikin 17 na jihar Filato yayin da PDP ta lashe kananan hukumomi guda shida.

    Filato na cikin jihohin da suka ja hankali ake karasa zabukan gwamnoni wadanda suka hada da Bauchi da Benue da Kano da kuma Sokoto.

  17. Mutum 10 sun mutu a wurin bikin addini a Habasha

    'Yan kallo bikin addini a kasar Habasha

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Benen ya rufta da 'yan kallo ne ana tsaka da biki

    Akalla mutum 10 ne suka mutu a wurin wani bikin addini sannan sama da 100 suka jikkata bayan wani bene na katako da 'yan kallo ke kai ya rushe a garin Gondar na kasar Habasha wato Ethipia, a cewar rahoton AFP.

    "Ina shaida maku cewa zuwa yanzu gawar mutum 10 muka samu. Wadanda suka rasu kuma sun kai 100 ko ma 150," in ji wani likita a asibitin Jami'ar Gondar.

    Bikin na kwana biyu wanda aka fi sani da Timket a harshen Amharic, ana tunawa da baftisimar da aka yi wa Yesu Almasihu a Kogin Jordan.

    Garin Gondar wuri ne mai tarihi wanda fadar gwamnatin Ethiopia ta taba zama a ciki, ana yi masa kallon cibiyar bikin, inda tikitin jirgin sama zuwa garin ke karewa da wuri saboda rubibin zuwa.

    Ga wasu hotuna da aka dauka na bikin gabanin tsautsayin:

    Masu bikin Timket a Ethiopia
    Masu bikin Timket a Ethiopia
    Masu bikin Timket a Ethiopia
  18. Alkalan sun koma kotu bayan hutu mai tsayi

    Alakai

    An ci gaba da da shari'a a kotun koli bayan da alkalan suka koma zama. Sai dai alkalan sun nemi gafarar jama'a bisa dan lokacin da suka kwashe ba su koma zaman ba.

    Kuma yanzu haka an fara shari'ar jihar Plateau, inda aka fara karanto hakunci.

    Kotun koli
    Bayanan hoto, Yadda jama'a suka yi jingun-jingum ke nan kafin komawar alkalan daga hutu
  19. Abba Gida-gida ya mayar da martani

    Abba Kabir Yusuf

    Mutumin da kotun kolin Najeriya ta ce ba shi ne ya yi nasara ba a zaben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana rashin nasarar tasa da kotun kolin ta tabbatar da " yunkurin wani gungun mutane da manufar lalata tsarin dimokradiyyar Najeriya".

    Maa magana da yawun Abba Kabir, Sunusi Bature Dawakin Tofa, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce "bisa la'akari da irin dumbin shaidu da aka gabatar da kuma gogaggun lauyoyi ya nuna irin halayyar zalunci ta yi wa jama'ar Kano fashi da makamin kuri'unsu.

    To sai dai sanarwar ta kara da cewa "mun ga irin tasu shari'ar abin da ya rage shi ne shari'ar Allah ubangiji da babu makawa sai an yi ta."