A ranar Litinin ne aka sa ran Kotun Koli a Najeriya za ta yanke hukunci kan kararrakin zabukan gwamna na jihohin Kano da Sokoto da Bauchi da Benue da Filato.
A Kano dan takarar gwamna na PDP ne dai Abba Kabir Yusuf ke kalubalantar nasarar da Abdullahi Umar Ganduje ya samu a zaben bayan da kotun sauraren kararrakin zabe ta jihar Kano da kuma kotun daukaka kara a Kaduna suka yi watsi da kararrakin da ya kai.
Yayin da shi kuma Ahmad Aliyu Na APC yake kalubalantar nasarar da Aminu Waziri Tambuwal na PDP ya samu shi ma a zaben inda daga baya kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar, da kuma kotun daukauka kara a Kaduna suka yi watsi da kararrakin da ya kai gabansu.
A jihohin Kano da Sokoto dai sai da aka je zagaye na biyu a zaben gwamnan jihohin da aka gudanar a bara.
Akwai kuma shari'a tsakanin Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad na jam'iyyar PDP da kuma Mohammed Abdullahi Abubakar na jam'iyyar APC.
Sai kuma akwai shari'a tsakanin Samuel Ortom na jam'iyyar PDP da kuma Emmanuel Jime na jam'iyyar APC daga Benue, sai kuma na jihar Filato tsakanin Jeremiah Useni na jam'iyyar PDP da kuma Simon Bako Lalong na jam'iyyar APC.
A makon da ya gabata ne dai kotun ta yanke hukunci kan zaben Imo inda ta kori Emeka Ihedioha daga gwamnan jihar ta bai wa Hope Uzodimma na jam'iyyar APC.