Gwamnati ta gargadi 'yan Najeriya kan cutar Coronavirus

Wannan shafi yana kawo maku irin wainar da ake toyawa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da Ghana da sauran kasashen Afirka da ma fadin duniya.

Rahoto kai-tsaye

  1. Kotu ta hana yi wa Musulmin Rohingya kisan kare-dangi

    Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta bayar da umarnin daukar matakan kare Musulman Rohingya daga kisan kare-dangi a kasar Myanmar da a baya ake kira (Burma).

    An yanke shawarar hakan ne duk da cewa jarogar gwamnatin kasar, Aung San Suu Kyi, ta kare kasarta da kanta kan zarge-zargen a watan jiya.

    Dubban ‘yan Rohingya sun mutu, sannan fiye da mutum 700,000 sun tsere zuwa Bangladesh a lokacin da sojoji suka far masu a 2017.

    Masu bincike na Majalisar Dinkin Duniya sun yi gargadin cewa za a iya sake samun irin wannan kisan kare-dangin.

    Karar, wadda kasar Gambiya ta shigar a kotun, ta yi kira da a dauki matakan gaggawa kan sojojin Myanmar har sai an gudanar da cikakken bincike.

    Myanmar ta sha dagewa cewa sojojinta na yakin magance masu tsattsauran ra’ayi ne a jihar Rakhine.

    A takarda da ta fitar na kariya kan karar a babban kotun Hague, Aung San Suu Kyi, ta kwatanta rikicin a matsayin ‘’yakin cikin gida’’ da ‘yan ta’addan Rohingya suka kai hare-hare kan wuraren aikin jami’an tsaron gwamnati.

    Dubban ‘yan Rohingya sun mutu, sannan fiye da mutum 700,000 sun tsere zuwa Bangladesh a lokacin da sojoji suka far masu a 2017.

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Dubban ‘yan Rohingya sun mutu, sannan fiye da mutum 700,000 sun tsere zuwa Bangladesh a lokacin da sojoji suka far masu a 2017.
  2. An bukaci ‘yan jarida su kula da labaran da za su yada ganain zabe a Kamaru

    Hukumomi a jamhuriyyar Kamaru sun kara jan hankulan manema labarai game da irin labarun da suke yadawa kan yakin neman zabe, a lokacin da ya rage makonni kwana biyu a fara yakin neman zabe na ranar tara ga watan Fabrairu a kasar.

    Wadannan kiraye-kiraye na hukumomi na zuwa ne a lokacin da kungiyar masu fafutuka da ke yunkurin kafa kasar Ambazoniya ke barazana a kan yiyuwar zabukan.

    Har ila yau, akwai wasu jam’iyyun siyasa da hukumomi ke cewa manufarsu ita ce su rinjayi magoya bayansu kada su fita su kada kuri’a.

    Sai dai tuni manema labarai suka fara kokawa kan yunkurin sanya takunkumi da hukumar kula da harkokin sadarwa take da nufin yi.

    Paul Biya ya zama shugaban Kamaru a 1982

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Paul Biya ya zama shugaban Kamaru a 1982
  3. Biloniya zai biya likitocin Zimbabwe albashin da gwamnati ta kasa biya

    Likitocin Zimbabwe sun amince da komawa bakin aikinsu bayan karbar tayin kudin da wani bilioniya ya yi musu, bayan shafe tsawon lokaci suna yajin aiki.

    An shafe fiye da wata hudu ana yajin aikin wanda suka fara shi sakamakon rashin biyansu albashi mai kyau da rashin kyakkyawan yanayin aiki, abin da ke lalata harkar lafiyar kasar.

    A shekarar da ta gabata ne wani biloniyan dan kasuwa mai kamfanin sadarwa Strive Masiyiwa, ya gabatar da bukatarsa ta shiga lamarin don kawo karshen yajin aikin.

    Mista Masiyiwa ya ce zai bayar da miliyan 100 na dalar Zimbabwe, wanda ya yi daidai da miliyan 6.25 na dalar Amurka.

    Ya ce zai biya kusan likitoci 2,000 wani alawus na kusan dalar Amurka 300 duk wata, don taimaka musu da kudin zirga-zirga da na yau da kullum.

    Biloniyan wanda ke zama a Birtaniya, zai biya likitocin kudin wata shida ta hanyar wata gidauniyarsa ta tallafi.

    Sai dai babu tabbas kan ko me zai faru bayan wata shidan.

    A wata sanarwa da ta fitar, kungiyar likitoci ta Zimbabwe ta tabbatar da cewa ta karbi tayin Mista Masiyiwa.

    Sai dai gwamnatin Zimbabwe wacce ta ce ba za ta iya kara albashin likitocin ba, ba ta ce komai ba kan tayin biloniyan har yanzu.

    Mista Masiyiwa ya ce zai bayar da miliyan 100 na dalar Zimbabwe, wanda ya yi daidai da miliyan 6.25 na dalar Amurka.

    Asalin hoton, Getty Images

  4. Gwamnatin Najeriya ta ja hankalin 'yan kasar kan cutar Coronavirus

    Gwamnatin Najeriya ta shawarci ‘yan kasar da ke tafiye-tafiye zuwa Wuhan a China da su kaucewa mu’amala da mutanen da ke nuna alamun rashin lafiya.

    Gwamnatin ta yi wannan gargadi ne sakamakon bullar kwayar cutar Coronavirus wadda ta samo asali daga birnin na Wuhan.

    A shafinta na Twitter, gwamnatin ta bukaci mutane su guji kusantar dabbobi masu rai ko mara rai da kuma kasuwannin dabbobi.

    Gwamnatin ta ce ma’aikatar lafiya ta hannun hukumar dakile yaduwar cututtuka da sauran hukumomin lafiya na kara kaimi wajen dakile barkewar cutar a sassan kasar.

    A cewarta, hukumar dakile bazuwar cututtuka na yin nazari kan illar shigo da kayayyaki daga wasu kasashen zuwa Najeriya.

    Hukumar kuma tana tatatunawa da hukumar lafiya da duniya WHO, kan yadda za a shawo kan lamarin.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  5. Ana zargin macen da ta fi kudi a Afirka da laifin cin hanci

    Masu shigar da kara a Angola sun fara tuhumar matar da ta fi kudi a Afirka, Isabel Dos Santos, da cin hanci a hukumance.

    Babban lauyan gwamnatin Angola, Helder Pitta Gros, ya ce zarge-zargen suna da da alaka ne da lokacin da take shugabantar kamfanin mai a kasar mai suna Sonangol.

    Ana kuma zargin wasu mutanen tare da Ms Don Santos.

    Mista Pitta Gros ya ce za a bayar da sammacin kama duk wadanda ake zargi a ko ina a duniya, idan ba su kawo kansu ga hukumomin Angola ba.

    Ana zargin Isabel do Santos da almubazzaranci da da dukiyar kasa a lokacin da take shugabantar Sonangol. Sai dai ta musanta zargen-zargen.

    Isabel do Santos da almubazzaranci da da dukiyar kasa a lokacin da take shugabantar Sonangol.

    Asalin hoton, Google

  6. Manoman a Sokoto shinkafa na na san barka da rufe kan iyaka

    Manoman shinkafa da 'yan kasuwa a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya sun ce sam barka domin sun ga tasirin hana shigo da shinkafa da rufe kan iyakoki da gwamnati ta yi.

    Sai dai kuma sun koka kan yadda ake fasa kaurin shinkafa ‘yar waje a cikin jihar mai makwabtaka da Nijar, dalilin da suka ce ke sa kasuwar shinkafa ‘yar gida ke ja da baya.

    A hannu guda su kuma mutanen gari kokawa suke da tsadar farashin shinkafar 'yar gida da aka gyare aka cirewa tsakuwa.

    Manoman shinkafa
  7. Barka da warhaka

    Muna yi muku barka da warhaka. Barka da sake saduwa a shafinmu na BBCHausa.com da ke kawo muku irin wainar da ake toyawa a Najeriya da Nijer da Kamaru da Chadi da Ghana da ma sauran sassan Afirka da duniya. Da fatan yau ma za ku kasance da mu tsawon wannan rana ta Alhamis.

  8. Kammalawa

    Masu bibiyarmu nan za mu karkare kawo rahotanni kai tsaye na yau Laraba. Da fatan za ku ci gaba da kasancewa tare da mu a gobe Alhamis idan Allah ya kai mu.

  9. Abincin da Shugaban Uganda yake ci da ya rage masa nauyin 30kg

    Yoweri Museveni

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Yoweri Museveni

    Rogo da dankalin Turawa da kuma kayan marmari na kasar Uganda, su ne suka sa shugaban kasar Uganda, Yoweri Museveni ya rage nauyin 30kg, kamar yadda ya shaida wa BBC da kansa.

    "A kodayaushe garau nake ji na amma likitoci sun nuna mani kuskuren da nake yi, saboda haka na yanke shawarar in canza salo don rage nauyi," in ji Mista Museveni.

    Shugaban mai shekara 75 ya ce kafin yanzu ba ya lura da nauyinsa, abin da ya sa ya kai har 106kg.

    Sannan ya karyata wasu maganganu da ake yi a shafukan sada zumunta cewa "jikinsa yana nuna gajiya", inda ya ce yana sane, nauyi kawai ya rage.

    A wani shafinsa na musamman a intanet, ya fada a watan da ya gabata cewa "ya kyale jikinsa ya yi kiba ne saboda likitoci ba su bayyana mana illar yin kiba ba".

    Ya kara da cewa nauyinsa a yanzu (76kg) shi ne mafi dacewa da mutum mai tsawonsa na kafa 5 (170cm).

    Sai dai bai bayyana tsawon lokacin da ya dauka ba kafin ya rage 30kg.

  10. Bola Tinubu ya ce ba a fahimci Amotekun ba

    Bola Ahmed Tinubu

    Asalin hoton, OTHERS

    Jagoran jam'iyyar APC mai mulkin kasar, Asiwaju Bola Tinubu wanda ya nemi zama da gwamnonin yankin kudu maso yamma da kuma atoni janar kuma ministan shari'a na kasar, Mallam Abubakar Malami don tattaunawa kan batun Amotekun, ya ce akwai matsalar rashin fahimtar tsarin.

    A wata sanarwa mai dauke da sa-hannun Bola Tinubu da aka aike wa manema labarai, Jagaban ya ce kafa kungiyar tsaron ta Amotekun sam-sam ba barazana ba ce ga kasar tun bayan da gwamnonin yankin suka kafa ta a kokarinsu na magance matsalar tsaro a jihohinsu.

    A cewar sanarwar "batun Amotekun ya karade ko ina kuma ya ja hankalin kafafen yada labarai, ya shafi yadda gwamnatoci za su taimaka wajen bai wa al'umominsu tsaro. Wannan abun damuwa ne sai dai kuma an sanya siyasa cikinsa."

    Tsohon gwamnan na Legas ya kuma ce "wadanda suke ikirarin gwamnatin kasar na neman dankwafar da kudu maso yamma ne kawai ra'ayinsu suke fada."

    A baya-bayannan ne gwamnatin Najeriya ta soke kungiyar tsaro ta Amotekun da wasu jihohin shiyyar kudu suka samar.

    Tun bayan daukar wannan mataki dai, jama'a a kasar ke tofa albarkacin bakinsu game da lamarin inda wasu ke ganin matakin wani koma baya ne kuma yana iya zama matsala a kasar nan gaba.

  11. Mutum 36 sun mutu a harin ta'addanci a Burkina Faso

    Gwamnatin Burkina Faso ta ce an kashe mutane 36 a wani harin ta’addanci a yankin arewa ta tsakiya na kasar.

    An bayyana cewa wata kungiyar mayaka ce ta kashe mutane 32 a wata kasuwar kauyen Nagraogo a yammacin Litinin, sannan suka kara kashe mutum hudu a yayin wani ahri kusa da garin Alamou.

    A ranar Talata, majalisar dokokin kasar ta kada kuri’a ka samar da masu aikin sa-kai domin yakar kungiyoyin ta’addanci.

    Kafafen yada labarai na cikin gida sun ruwaito cewa za a bai wa masu aikin sa-kan horon farko irin na sojoji.

  12. Buhari ya yi Allah-wadai da kisan Reverend Lawan Andimi

    Buhari

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi Allah wadai da kisan wani shugaban addinin kirista a arewacin kasar.

    ‘Yan bindiga da ake tunanin masu da’awar kishin musulunci ne sun sace Reverend Lawan Andimi a farkon watan Janairu.

    Cikin wata sanarwa, shugaban kasar ya bayyana kisan Reverend Andimi a matsayin wani abu da aka yi da gangan.

    Ya kuma bayyana cewa masu garkuwar sun nuna alamun za su sake shi ta hanyar mika shi hannun wasu mutane.

    Sai dai ba su bayyana ko su wanene mutanen ba.

    Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International ta yi tur da kisan inda kuma ta bukaci hukumomi su kara kaimi wajen kubutar da mutanen da Boko Haram ta yi garkuwa da su.

    Kisan Reverend Andimi shi ne harin baya-bayan nan da masu da’awar kishin Musulunci a yankin suka kai kan mabiya addinin kirista.

    A watan Disamba ne masu ikirarin jihadi da ke da alaka da kungiyar IS suka fitar da wani hoton bidiyo da ke nuna yadda suka kashe kiristoci 11 a arewa maso gabashin Najeriya.

  13. Mutum 15 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a DR Congo

    DR Congo

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutane 15 sun mutu a wani hatsarin kwale-kwale da ya kife a wani tafki da ke gabashin Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo, a rahoton kamfanin dillancin labarai na AFP.

    An samu karin wasu mutane da su ka bace a hatsarin ranar Litinin na tafkin Mai-Ndombe, inji Magajin garin Inongo, Cosmos Mboo Wemba.

    Har yanzu dai ba a san mai ya haddasa hatsarin ba.

    Dan jarida Firoger Balimba, ya ce Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ce kwale-kwalen na dauke ne da kimanin mutane 30 da ke komawa daga jana’iza mai nisan kilomita 35.

    A watan Mayun 2019, akalla mutane 45 sun mutu a tafkin, bayan wani kwale-kwalen da ke dauke da fiye da mutane 400 ya nutse.

    Yawancin wadanda ke cikin kwale-kwalen malamai ne da za su je karbar albashinsu.

    Ana yawan samun hatsarin kwale-kwale a Demokradiyyar Congo, saboda daukar mutane fiye da kima da kuma rashin kula da kwale-kwalen.

  14. Wani biloniya zai biya likitoci albashi a Zimbabwe don su koma aiki

    Strive Masiyiwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Strive Masiyiwa

    Likitoci a kasar Zimbabwe sun amince su koma bakin aiki bayan wani yajin aiki na kusan wata hudu sakamakon yarjejeniyar da suka yi da wani biloniyan dan kasuwa mai harkokin sadarwa a kasar.

    Yajin aikin yana daya daga cikin wanda ya fi kowanne tsayi a tarihin kasar sannan kuma ya durkusar da bangaren lafiyar kasar.

    Biloniyan wanda da ke zaune a Birtaniuya, Strive Masiyiwa zai biya kowane likita alawus na dala 300 (Naira 108,600) da kuma taimakon sufuri zuwa wurin aiki bisa doron wata gidauniya da ya kafa.

    Mafi yawan likitocin da suke yin yajni aikin, wadanda kanana ne, suna karbar albashin dala 100 ne (Naira 36,200) a wata.

    Dan kasuwar zai biya likitocin na tsawon wata shida amma babu tabbacin abin da zai faru bayan haka.

    Yajijn aikin ya halaka mutanen da ba a san adadinsu ba, in ji kungiyar manyan likitocin kasar wadanda suka kira shi (yajin aikin) da cewa "kisan kare-dangi ne a fakaice".

    Likitocin sun tafi yajin aikin ne bisa bukatar da suka gabatar ta a rika biyan su da dalar Amurka sakamakon tashin farashin kayayyaki mafi muni a tarihin kasar.

  15. Saudiyya ta musanta zargin yi wa Jeff Bezos kutse

    Yariman Saudiyya

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomin Saudiyya sun musanta zargin da ake yi wa yariman kasar, Muhammad Bin Salman na kutsa wa wayar hamshakin dan kasuwar nan mamallakin kamfanin Amazon wato Jeff Bezos.

    Ofishin jakadancin kasar a Amurika ya bayyana zargin a matsayin mara tushe ballantana makama, tare da bukatar aiwatar da bincike domin tabbatar da gaskiyar lamari.

    Dangantaka ta yi tsami tsakanin Saudiyya da dan kasuwar wanda kuma shi ne mamallakin fitacciyar jaridar nan ta Amurika wato 'Washington Post' bayan kisan daya daga cikin marubutanta Jamal Khashoggi da ake zargin Yariman da yi.

    An kutsa wayar dan kasuwar ne bayan samun wani sako ta WhatsApp dinsa a watan Mayun 2018, kuma Yariman Saudiyyan Muhammad Bin Salman ne ya aika masa da sakon kamar yadda jaridar Guardian ta rawaito.

    Wani bincike da aka kaddamar dangane da laifin kutsen da ya saba wa ka'idar bayanan sirri ya nuna cewa jim kadan bayan latsa mashigin wani bidiyo da Yariman ya aika masa sai kawai wayar ta fara fitar da dumbin bayanan sirrin da aka jibga mata.

    Saudiyya dai ta musanta zargin.

  16. 'Jahilci ne yake kawo rikice-rikicen addini a addini a Najeriya'

    Sanusi Lamido Sanusi

    Sarkin kano Mai martaba Sanusi Lamido Sanusi ya ce matsalar jahilci ce ke jawo rikice-rikicen addini a Najeriya tsakanin musulmai da kiristoci.

    Sarki Sanusi, wanda ya wakilci Sarkin Musulmin Najeriya a wani taron neman mafita kan rikice-rikicen addini a Najeriya, da ke gudana a birnin Abuja, ya ce a tarihin musulunci musulmai sun taba zuwa hijira wajen shugaban kiristoci a kasar habasha.

    Shi ma a nasa jawabin, Rabaran Mathew Hassan Kuka ya ce ya yi kisan jama’ar da ake yi a Najeriya ya isa haka inda ya nemi da a hada hannu a tunkari gwamnati domin ta dakatar da hakan.

    Sarki Sanusi ya kara da cewa yadda “ake yada labaran karya a kafaffen sadarwa na daga cikin abubuwan da suke kara ta'azzara rikice-rikicen addini.”

    Sarki Sanusi da Rabaran Hassan Mathew Kuka
    Wani bangaren mahalarta taro
  17. MURIC ta yi Allah-wadai da kisan shugaban CAN a Adamawa

    Lawan Andimi

    Asalin hoton, Family

    Bayanan hoto, Lawan Andimi

    Kungiya mai kare hakkin Musulmi a Najeriya ta Muslim Rights Concern (MURIC) ta yi Allah-wadai da kisan shugaban kungiyar Kiristoci ta CAN, wanda ake zargin kungiyar Boko haram da aikatawa a jihar Adamawa.

    An halaka Lawan Andimi ne a karamar hukumar Michika, abin da MURIC ta bayyana shi da "rashin imani da kuma keta".

    A ranar Talata ne Mista Nicholas, wanda da ne ga marigayin, ya tabbatar wa BBC da mutuwar mahaifinsa, amma ya ce ba zai iya wani karin bayani ba domin suna cikin alhini da makoki.

    An dai yi garkuwa da shugaban kungiyar ne a farkon watan Janairun wannan shekara a wani hari da 'yan kungiyar Boko Haram suka kai a kauyensu.

    Kwanaki kadan bayan da aka yi garkuwa da shi, an ga marigayin a wani bidiyo da 'yan kungiyar Boko Haram din suka saki, inda aka ga malamin addinin yana rokon gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Fintiri ya ceci rayuwarsa.

    A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, babban daraktan kungiyar MURIC Farfesa Ishaq Akintola ya ce "duk wanda ya kashe wani mutum ba tare da laifin komai ba to ba Musulunci yake wakilta ba," kamar yadda kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito shi yana fada.

    "Babu abin da za mu iya kwatanta wannan kisan da shi, rashin imani ne kawai da kuma keta.

    "Mun yi Allah-wadai da shi ta kowace fuska sannan kuma muna kara jaddada matsayinmu cewa Boko Haram ba kungiyar Musulunci ba ce, hasali ma ta wadanda suka bata ce.

    "Muna kira ga 'yan Najeriya da su hada kansu su yaki Boko Haram ba tare da bambancin addini ba kuma su kori shaidanu daga cikinsu."

  18. 'Yan al-shabab sun sa malam makaranta gudu a yankin Garissa na Kenya

    Al-shabab

    Asalin hoton, Getty Images

    A Kenya gwamman malaman makaranta da ke Garissa ke fafutukar barin yankin don tsira da ransu. Mayakan Alshabab sun kaddamar da hare-hare shidda a makonni biyar tun daga watan Disamba a Kenya, inda suka kashe sama da mutum ashirin da biyar kuma sun yi barazanar kara kai hare-hare.

    A yankin Garissa malamai uku da dalibai uku aka kashe a harin, kuma gwamnati na cewa tana karfafa tsaro don kawo karshen lamarin.

  19. Rashford zai kwashe makonni shida kafin ya koma atisaye - Solskjaer

    Marcus Rashford

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Manchester United Ole Gunnar Solskjaer ya ce kulob din zai bai wa dan wasan gabansa Marcos Rashford isasshshen lokacin da yake bukata domin farfadowa daga raunin da ya samu.

    Zuwa yanzu babu wanda ya san tsawon lokacin da dan wasan mai shekara 22 zai kwashe yana jinyar raunin da ya samu, kana kungiyar ta ki bayar da tabbacin cewa ko dan wasan zai iya murmurewa kafin karewar kakar wasa ta bana.

    Tabbacin da Solksjaer ya bayar kawai shi ne Rashford zai iya shafe tsawon makwanni shida nan gaba kafin ya dawo atisaye.

  20. Saura kiris a bai wa hammata iska a majalisar dokokin Amurka kan Trump

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dattawan Amurka ta amince da wasu ka'idoji da aka gindaya kan fara sauraron shari'ar da za ta iya kai wa ga tsige Shugaba Donald Trump, bayan kusan shafe sa'oi 13 ana tafka muhawara a ranar farko.

    Saura kiris masu gabatar da kara na jam'iyyar Democrat su gwada kwanji da lauyoyin Trump game da zaman sauraren shari'ar yayin da 'yan Republican suka nuna kin amincewarsu da bukatar a gabatar da shaidu fiye da daya.

    Trump shi ne shugaba na uku da ya taba fuskantar barazanar tsigewa daga kan karagar mulki.

    Ana tuhumar sa da yin gaban kansa da kuma yi wa yunkurin majalisa na gudanar da bincike karen tsaye amma ya musanta zargin.

    Trump dai na fuskantar irin wannan shari'a ce bayan da majalisar wakilan kasar ta tsige shi a watan daya gabata sakamakon samun sa da laifin aikata laifukan da aka zarge shi da aikatawa.