Ƴan ƙwallon Uganda 11 da za su fuskanci Najeriya

Asalin hoton, gett
Wannan shafi ne da zai ke kawo muku bayanai kan wasan Uganda da Najeriya da na Tanzaniya da Tunisia a gasar kofin nahiyar Afirka ta 2025 da ake yi a Moroko.
Mohammed Abdu

Asalin hoton, gett

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, BBC Sport

Asalin hoton, BBC Sport

Asalin hoton, Getty Images
Idan har Tunisiya ta kai zagayen gaba zai zama karo na 15 kenan za ta buga wasanin yan 16.
An yi waje da Tunisia a karawar cikin rukuni a 2023, rabon da ayi waje da ita a gasa biyu a jere daga cikin wasannin rukuni tun 1982 da kuma 1994.
A gasar Afcon biyar baya da suka halarta, sau daya ne aka yi waje da ita a zagayen cikin rukuni, shi ne a 2023.
Kwallon farko da Super Eagles ta ci Tunisiya ita ce ta 100 da aka zura a ragarta a tarihin Afcon.
Kenan Tunisiya ta zama ta biyu da aka ci kwallo 100 ko fiye da haka a Afcon bayan Ivory Coast.

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, Getty Images
Ta fara wasan bana a Afcon da rashin nasara 2-1 a hannun Super Eagles da kuma tashi 1-1 da Uganda a karawar cikin rukuni na uku.
Har yanzu Tanzania ba ta ci wasa ba daga 11 da ta buga a Afcon, wadda tasha kashi karo bakwai da canjaras hudu daga ciki.
Idan har ba ta yi nasara ba ranar Talata za ta zama ta hudu da ta kasa cin wasa daga karawa 12 ko fiye da hakan a Afcon, bayan Mozambique karawa 16 da Benin wasa 15 da kuma Guinea-Bissau mai fafatawa 12.
A tarihin wasan karshe a cikin rukuni a Afcon ta buga fafatawa uku da rashin nasara daya da canjaras biyu.
Ba a doke ta ba a wasan karshe a cikin rukuni a Afcon karo biyu baya, wadda ta tashi 1-1 da Ivory Coast a 1980 da kuma 0-0 da Jamhuriyar Congo a 2023.
Wasan bayan nan da ta yi rashin nasara a karawar karshe a rukuni shi ne 3-0 da Algriya ta ci a 2019.

Asalin hoton, Getty Images
Jimilla sun kara sau takwas tsakaninsu a dukkan fafatawa. Uganda ta yi nasara huɗu, Najeriya ta ci wasa biyu da canjaras biyu
Haka kuma an haɗa rukuni tare da Uganda da Najeriya a wasan neman shiga gasar cin kofin Afirka na 1994 da kuma na 2008.
A wasa huɗu da za su kara kenan gida da waje Najeriya ta yi nasara biyu, Uganda ta ci ɗaya da canjaras ɗaya - Kuma Super Eagles ce kan kai bante zuwa gasar.
Wasan baya-bayan nan da suka haɗu shi ne na sada zumunta ranar 20 ga watan Nuwamba da aka tashi canjaras a Asaba a jihar Delta a Najeriya.
Kawo yanzu a wasa uku ba a doke Uganda ba a karawa da Najeriya, wadda ta yi nasara biyu da canjaras ɗaya.
Wasan karshe da Super Eagles ta ci Uganda a Afcon a wasan neman shiga gasar 2008 ta ci 1-0 ranar 24 ga watan Maris 2007 a filin MKO Abiola a Abeokuta, inda Nwankwo Kanu ne ya zura ƙwallon a raga a minti na 73.

Asalin hoton, Getty Images
Ta fara gasar bana da yin nasara 3-1 a kan Uganda daga baya ta sha kashi 3-2 a hannun Super Eagles a wasa na biyu a rukuni na uku.
Karon farko da ta yi rashin nasara a Afcon duk da cin kwallo biyu da ta yi tun bayan doke ta da Kamaru ta yi 3-2 a kwata fainal a 2008.
Kafin shan kashi a hannun Najeriya, Tunisiya ta yi karawa tara a Afcon ba tare da an doke ta ba da zarar ta ci kwallo biyu ko fiye da hakan daga ciki ta lashe wasa takwas da canjaras daya.
Wasa takwas ta yi nasara a jere da zarar ta ci kwallo biyu ko fiye da haka daga baya ta yi rashin nasara a hannun Najeriya.
Ta kasa cin wasa na uku a cikin rukuni a karawa uku baya a Afcon daga ciki ta tashi 0-0 da Mauritania a 2019, sannan ta yi rashin nasara 1-0 a hannun Gambia, da kuma tashi 0-0 da Afirka ta Kudu a 2023.
Wasan da ta ci na karshe a cikin rukuni shi ne a 2017, inda ta ci Zimbabwe 4-2.

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, Getty Images
Uganda da Najeriya za su fuskanci juna a karo na biyu a gasar cin kofin nahiyar Afirka, bayan da za su kara a fafatawa ta uku-uku a rukuni na uku ranar Talata a Complex Sportif de Fes.
Wasa tilo da suka fuskanci juna a Afcon shi ne a zagayen daf da karshe a 1978, inda Uganda ta yi nasarar cin Najeriya 2-1
A karawar da suka yi a 1978 a daf da karshe, Uganda ta fara cin ƙwallo ta hannun Abdulla Nasur a minti na 11 daga baya Najeriya ta farke ta hannun Martins Eyo a zagaye na biyu.
Sai dai daf a tashi ne Phillip Omondi ya ci wa Uganda na uku da ya kaita zagayen gaba.

Asalin hoton, Getty Images
Filin wasa na Stade Prince Moulay Abdellah Olympique Annexe a Rabat zai karbi bakuncin wasan karshe a rukuni na uku tsakanin Tanzania da Tunisia ranar Talata.
Dukkansu tawagogin na neman gurbin kai wa zagaye na biyu a gasar cin kofin Afirka da ake yi a Morocco.
Wannan shi ne karon farko da za su fafata tsakanin Tanzania da Tunisiya a Afcon.
A wasan baya da suka kara a neman shiga Afcon na 2021, Tunisiya ce ta yi nasara a wasan farko 1-0 a Rades ranar 13 ga watan Nuwambar 2020, inda Youssef Msakni ya ci kwallon.\
A wasa na biyu a Dar Es Salam ranar 17 ga watan Nuwambar 2020 suka yi 1-1, kuma Saïf-Eddine Khaoui na Tunisiya ne ya fara cin kwallo a minti na 11 daga baya Feisal Salum na Tanzania ya farke a minti na 48.
Tunisia ce ta samu gurbin Afcon a 2021, yayin da Tanzania ta zama yar kallo.
Wannan shi ne karo na hudu da Tanzaniya za ta kece raini da tawaga daga Arewacin Afirka a Afcon, kuma duk rashin nasara ta yi a uku baya - Masar ta ci 2-1 a 1986 da Aljeriya a ta doke ta 3-0 a 2019 da rashin nasara a hannun Morocco a 2023.
Idan har Tanzaniya ta kai zagaye na biyu zai zama a karon farko, bayan da ta kasa kai bante zuwa zagayen yan 16 a Afcon a 1980 da 2019 da kuma 2023.

Asalin hoton, Getty Images
Oswin Appollis ne ya zura kwallo a bugun fenareti a cikin mintuna 10 na karshe, wanda ya bai wa Afirka ta Kudu nasarar doke Zimbabwe 3-2 a wasan da suka yi a Marrakech ranar Litinin.
Hakan ya sa ta kare a mataki na biyu a teburi a rukuni na biyu, ta kuma yi waje da takwararta daga Kudancin Afirka daga gasar Afcon da Morocco ke shiryawa.
Afirka ta Kudu ta kammala a mataki na biyu a rukuni da maki shida da tazarar daya kacal tsakani da Masar, wadda ita ce ta ja ragamar rukuni.
Ita kuwa Angola ta yi ta uku da maki biyu, za ta jira ko hakan zai sa ta kai zagaye na biyu daga tawaga hudu da za a dauka da suka yi na uku a cikin rukuni da maki mai kyau.

Asalin hoton, Getty Images
Mali da Comoros sun tashi ba ci a gasar cin kofin Afirka a rukunin farko da suka kara ranar Litinin a Casablanca.
Da wannan sakamakon Mali ta kai zagayen yan 16 kai tsaye, an kuma yi waje da abokiyar hamayyarta daga Afcon na bana.
Mali ta kare a mataki na biyu a rukunin farko da maki uku, bayan canjaras a wasa uku, biye da mai masaukin baki, Morocco mai maki bakwai daga karawa uku.
Comoros, wadda ta kare a mataki na uku mai rarar kwallaye biyu da ake binta, kenan ba ta daga cikin tawaga hudun da za a zaba, domin shiga wasannin zagaye na biyu
Amma dai Mali za ta kara da duk wadda ta yi ta biyu a rukuni na biyu inda ranar Talata ake sa ran sanar da wadda za ta kara da ita - amma dai ana hasashen Tunisia ce.
Sai dai Mali za ta buga wasan zagayen gaba ba tare da Amadou Haidara ba, saboda jan katin da aka yi masa a karawa da Comoros ranar Litinin kan cewa ya yi keta mai muni.

Asalin hoton, Getty Images
Dan wasan gaban Morocco, Ayoub El Kaabi ne ya ci kwallo biyu, yayin da gwarzon nan mai taka leda daga tsakiya Brahim Diaz ya kara daya a raga , yayin da masu masaukin baki a gasar AFCON suka doke Zambia da ci 3-0 a ranar Litinin, sun kuma kare a saman teburi a rukunin farko.
Morocco ta kammala wasa uku a cikin rukuni da maki bakwai, gaba da Mali da ke matsayi na biyu da maki uku.
Bayan da ta fara gasar cikin shakku — ta fara da yin nasara da kyar da karamar kasar Comoros, sannan ta yi kunnen doki 1-1 da Mali a ranar Juma’a — a wasan karshe na uku a cikin rukuni, Morocco ta nuna da gaske take yi, tana daga cikin tawaga 24 da ake hasashen za ta iya lashe kofin.
Da wannan sakamkon an yi waje da Zambia a gasar bana, bayan da ta kare a matakin karshe da maki biyu kacal.

Asalin hoton, Getty Images
Masar ta hutar da manyan yan wasanta, amma ta ci gaba da wasa ba tare da an doke ta ba a gasar cin kofin nahiyar Afirka, wadda ta tashi 0-0 da Angola - kenan ita ce ta farko a teburin rukuni na uku da maki bakwai.
Tun kan take wasan Masar ta kai zagaye na biyu, hakan ya sa ta canja yan wasa 11 daga wadanda suka ci Afirka ta Kudu 1-0 ranar Juma'a a karawa ta biyu a rukuni na biyu, inda Mohamed Salah da Omar Marmoush suka huta.
Angola ta kare a mataki na uku a rukunin, sannan za ta jira ta ji ko za ta samu damar kaiwa zagaye na biyu na yan tawaga 16 daga cikin hudun da za a zaba daga wadanda suka kare a mataki na uku da maki mai kyau.
Bayan da aka ci Zambia, sannan Comoros ta tashi 0-0 a wasan rukunin farko, kenan watakila ta bai bante idan aka ci Uganda da Tanzania ranar Talata.

Asalin hoton, Getty Images
Pierre-Emerick Aubameyang ya kammala buga gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Morocco, bayan da ya koma Faransa a ranar Talata kenan ba zai buga wa Gabon wasan karshe ba a gasar.
Bayan shan kashi a wasa biyu a rukuni na shida a hannun Kamaru da Mozambique, Gabon ta fice daga gasar duk da akwai wasa daya da ya rage mata, wanda za ta fafata da mai rike da kofin, Ivory Coast, a Marrakech ranar Laraba.
Mai shekara 36, an sa ran cewa wasa da Ivory Coast zai kasance na karshe da zai yi wa kasarsa a shekaru 16 yana wakiltarta, sai dai yanzu haka ya koma ƙungiyarsa ta Olympique de Marseille.

Asalin hoton, Getty Images