Fifa na kokarin ganin Iran ta buga gasar kofin duniya a bana, Fifa World Cup

Asalin hoton, Getty Images
Gwamnatin Iran ta ce ba za ta yanke hukunci kan halartar tawagar ƙasarta a gasar FIFA World Cup ba sai bayan ta samu amsa daga FIFA dangane da bukatar canza wurin wasannin ta.
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Iran (FFIRI) na ƙoƙarin a mayar da wasannin rukuni da take ciki daga Amurka zuwa Mexico, saboda dalilan tsaro da suka danganci rikicin siyasa a yankin.
A watan da ya gabata, FFIRI ta bayyana cewa tana tattaunawa da FIFA kan sauya wurin wasa, yayin da ma’aikatar wasanni ta Iran ta hana tawagar ƙasar da na ƙungiyoyinta zuwa buga wasa a ƙasashen da take kallon abokan gaba.
Sai dai shugaban FIFA, Gianni Infantino, ya sanar a makon da ya gabata cewa Iran za ta buga wasanninta kamar yadda aka tsara.
A halin yanzu, an tsara Iran za ta buga dukkan wasanninta na rukuni a Amurka – inda za ta kara da New Zealand da Belgium a Los Angeles, sannan ta kammala da wasa da Egypt a Seattle.
A gefe guda, shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Iran za ta iya zuwa Amurka domin buga wasa, amma ya nuna damuwa kan tsaron su, duk da cewa daga baya ya bayyana cewa duk wani barazana ba zai fito daga Amurka ba.





