Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 21/05/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 21/05/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Babangida da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Za a fara gwajin riga-kafin cutar sanyin goloriya a Birtaniya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Ingila za ta zama ƙasa ta farko a duniya da za ta fara yin gwajin riga-kafin cutar goloriya, wata cuta mai yaduwa ta hanyar saɗuwa

    Ba kowa ne za a yi wa riga-kafin ba. Za a mayar da hankali ne musamman kan maza masu luwaɗi da kuma waɗanda suka taba kamuwa da wata cuta ta jima’i.

    Riga-kafin yana da tasiri tsakanin kashi 30 zuwa 40 cikin 100, amma Hukumar Lafiya ta NHS England na fatan hakan zai taimaka wajen rage yawan sabbin kamuwa da cutar, wanda ke ƙaruwa cikin sauri.

    A shekarar 2023, an samu fiye da mutum 85,000 da suka kamu da goloriya– adadin mafi yawa tun da aka fara adana bayanai a shekarar 1918.

    Goloriya ba lallai ne ta nuna alamomi ba, amma daga cikin su akwai jin zafi yayin fitsari da kumburi da kuma iya haifar da rashin haihuwa.

    Ba a sani ba ko mutane da yawa za su amince a yi musu allurar riga-kafin ba.

    Asali, wannan rigakafin ba don cutar goloriya kaɗai aka kirkireshi ba harda riga-kafin cutar sankarau da ake yi wa jarirai a halin yanzu saboda kwayoyin cutar sanƙarau da na goloriya suna da alaƙa sosai.

  2. Harin Isra'ila ya kashe ƙarin mutum 15, har yanzu agaji bai isa jama'a ba a Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar agajin gaggawa da ke karkashin ikon Hamas ta bayyana cewa mutum 15 ne suka sake mutuwa a Gaza tun daga tsakar dare sakamakon hare-haren saman da Isra’ila ta kai.

    Waɗanda suka mutu a harin da aka kai a Jabalia, arewacin Gaza sun haɗa da mutum 11, inda wasu 13 kuma suka jikkata.

    Yayin da kuma a wani hari na dabam da aka kai wani gari, mutum biyu ne suka mutu tare da yaro ɗaya.

    Hukumar ta bayyana cewa waɗannan alkaluman na mutuwa daga tsakar dare ne zuwa yanzu, a lokaci na gida.

    ...

    Asalin hoton, Reuters / Cogat

    A halin da ake ciki kuwa, Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce har yanzu ba a raba kayan agaji a Gaza ba, duk da cewa an fara shigar da su bayan kawo ƙarshen kulle na makonni 11.

    Jami’an Isra’ila sun ce motoci 93 ɗauke da kayan agaji sun shiga Gaza a ranar Talata “bayan cikakken binciken tsaro”.

    Sai dai ofishin jinƙai na MDD ya ce an ajiye kayan ne kawai a ɓangaren Falasɗinawa na iyaka, ba a raba su ba.

  3. 'Arsenal na dab da ɗaukar ɗan wasan gaba Viktor Gyokeres'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Arsenal na shirin ɗaukar ɗan wasan gaban Sporting CP, Viktor Gyokeres kamar yadda jaridar wasanni ta football365 ta ruwaito.

    Arsenal ta fuskanci matsalolin ƴanwasan gaba a kakar wasan da ke dab da ƙarewa, yayin da ƙungiyar da gaza lashe kowane irin kofi.

    Bayan ƙarewa a mataki na biyu a Gasar Premier da samun gurbin zuwa Gasar Zakarun Turai ta baɗi a yanzu hankalin ƙungiyar ya karkata kan samun ɗan wasan gaba, domin sake gina kanta.

    A ƙarshen kakar wasa da muke ciki ne Gyokeres ɗan asalin Sweden zai bar ƙungiyar Sporting bayan ƙarewar kwantiraginsa, kamar yadda Fabrizio Romano fitaccen ɗanjaridar wasanni ya bayyana a shafinsa na X.

  4. Ana farautar fursunoni bakwai da suka tsere daga gidan yari a Osun

    ...

    Asalin hoton, NCoS

    Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce ta ƙaddamar da bincike tare da farauta mai zurfi domin kama fursunoni bakwai da suka tsere daga gidan gyaran hali da ke Ilesa a Jihar Osun, bayan ruwan sama mai ƙarfi da ya lalata tsaron wurin.

    Mai magana da yawun hukumar, Umar Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar da daren Talata.

    Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2 na dare, a ranar Talata, 20 ga watan Mayun 2025, inda hakan ya haifar da tserewar fursunoni bakwai.

    “Biyo bayan faruwar lamarin, shugaban hukumar gyaran hali na ƙasa, Sylvester Ndidi Nwakuche, ya bayar da umarnin gaggauta gudanar da bincike kan yadda fursunonin suka samu damar tserewa,” in ji sanarwar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa hukumar tana aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin kamo waɗanda suka tsere tare da mayar da su gidan yari.

    Hukumar ta kuma nemi haɗin kai da goyon bayan jama’a wajen bayar da duk wata bayani da zai iya taimakawa wajen kamo waɗanda suka tsere.

  5. 'An yi asarar Gandun daji mafi muni a tarihin duniya'

    ...

    Asalin hoton, Murray Lowe

    Sabbin alƙalumma sun nuna cewa an yi asarar gandun daji da dama a wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba a bara.

    Cibiyar kare Albarkatun Duniya ta ce sare dazuzzuka ya kusan ninka sau biyu, yayin da yankuna da dama a duniya ke ƙokarin shawo kan gobarar daji.

    Masu bincike sun ce ana asarar kwatankwacin filayen wasan kwallon kafa goma sha takwas a kowanne minti daya.

    Tsananin zafi ya haifar da ƙarin fari da haɗarin samun gobara.

    Masanan sun ce dazuzzukan da ke konewa na zuke iskar da ya kamata mu shaka maimakon su bamu ita.

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wanann rana ta Laraba, ta bawa ranar samu, kamar yadda Hausawa ke yi mata kirari.

    Barkanmu da sake gamuwa da ku a daidai wannan lokaci domin ci gaba da sake kawo muku halin da duniya ta wayi gari.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta irin su X da Facebook da Instagram domin karanta wasu labaran

    Ku kasance tare da mu.