'Za mu yi martani idan Amurka, Faransa da Birtaniya suka taimaka wa Isra'ila'
Iran ta yi gargaɗi Amurka, da Birtaniya da kuma Faransa kan cewa kada su kuskura su taimako wa Isra'ila kare kanta daga hare-haren da take kai wa, a cewar kafofin yaɗa labaran Iran.
Iran ta ce muddin haka ya faru za ta mayar da martani mai zafi.
Rahotanni sun bayyana cewa Tehran za ta afka wa sansanonin soji da jiragen ruwa da faɗin yankunan uku, in har suka taimaka wa Isra'ila.