Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 02/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sassan duniya kai tsaye - Asabar , 02/11/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Annur Muhammad da Abdullahi Bello

  1. Kamal Harris da Donald Trump za su fafata a jihar North Carolina

    ...

    Asalin hoton, ...

    A kwana na hudu a jere, Donald Trump da Kamala Harris za su yi yaƙin neman zaɓe a jiha guda, kwanaki kaɗan gabanin zaɓen shugaban ƙasar Amurka da za a yi ranar Talata mai zuwa.

    North Carolina ita ce jiha ta baya-bayan nan da za ta karɓi baƙuncin abokan hamayyar biyu.

    Ƴan jam'iyyar Republican na kallon jihar a matsayin wadda ta zame dole su lashe kuma suna matsa ƙaimi wurin tabbatar da cewa jami'iyyar Democrat ba ta bayar da mamaki ba.

    Cikin Shekara 50 da suka gabata Barack Obama ne kadai ɗan takarar jam'iyyar Democrat da ya taɓa lashe zaɓe a North Carolina

  2. Dakarun RSF sun kashe mutum 12 a arewacin Darfur

    mayaƙan RSF

    Asalin hoton, AFP

    Wasu rahotanni daga yankin Darfur na ƙasar Sudan na cewa dakarun RSF sun kashe aƙalla mutum 12 tare da raunata wasu biyar a hare-haren da aka kai a yankunan fararen hula.

    Wata ƙungiyar masu rajin kare dimokradiyya ta ce dakarun RSF - waɗanda suka shafe shekara guda da rabi suna yaƙar sojojin ƙasar - sun kai hari a yankin Kutum da ke Arewacin Darfur.

    Gwamnan yankin Darfur - Minni Minnawi - wanda ke goyon bayan sojoji - ya zargi ƙungiyar RSF da banka wa ƙauyuka kusan ashirin wuta.

  3. Ambaliyar Spain: Gwamnatin Sifaniya ta umarci jami'an tsaro fiye da 10,000 su koma Valencia

    masu ceto

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan sifaniya ya umarci sojojin ƙasar 5,000 da 'yansanda 5,000 da jami'an tsaron fararen hula su tafi yankin Valencia, yayin da mazauna yankin ke ci gaba da sukar gwamnati kan yadda ta ɗauki mummunar ambaliyar da ta addabi yankin.

    Pedro Sánchez ya tabbatar da mutuwar mutum 211 sakamakon bala'in, yayin da ake sa ran adadin zai ƙaru.

    Mamakon ruwan sama kamar da baƙin ƙwarya da aka fara tun a ranar litinin ya lalata gadoji tare da shafe garuruwa, lamarin da ya haddasa wa mazauna yankin rasa ruwan sha da abinci da wutar lantaki.

    Mista Sánchez ya ce tura jami'an tsaron, shi ne mafi girma da aka taɓa yi a cikin ƙasar, domin kai ɗauki kan ɗaya daga cikin mummunar ambaliya da ƙasar ta fuskanta cikin ƙarni guda.

    Firaministan ya ce yana sane cewa ''ɗaukin da gwamnatinsa ta kai yankin bai wadatar ba'', inda ya amince cewa an samu ''ƙarin matsaloli da rashin abubuwa masu yawa''.

  4. Kemi Badenoch: Mace ta farko baƙar fata ta zama shugabar jam'iyyar Conservatives ta Birtaniya

    ..

    Kemi Badenoch ta alƙawarta maido wa jam'iyyar Conservatives magoya bayanta da suka fice daga cikinta, bayan da ta kafa tarihin zama shugabar jam'iyyar a zaɓen shugabancin jam'iyyar da ka gudanar.

    Mai shekara 44 ta zama mace ta farko baƙar fata da za ta jagoranci babbar jam'iyyar siyasa a Birtaniya.

    Ta doke babban abokin karawarta Robert Jenrick bayan ta samu ƙuri'a 12,418, a fafatawar da aka ɗauki dogon lokaci ana gudanarwa domin zaɓar wanda zai maye gurbin, Rishi Sunak - mutumin da ya jagoranci babbar faɗuwar da jam'iyyar ta yi a tarihi a babban zaɓen da aka gudanar cikin watan Yuli.

    Cikin jawabin da ta gabatar bayan samun nasarar, Ms Badenoch ta alƙawarta ''sabunta'' jam'iyyar tare da shaida wa magoya bayan jam'iyyar cewa lokaci ya yi da za a ''farfaɗo da jam'iyyar''.

  5. Sojojin Najeriya sun kama wani ƙasurgumin ɗanbindiga da suke nema ruwa a jallo

    mm

    Asalin hoton, X/DEFENCE HQ

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun kama gawurtaccen ɗanbindigar nan mai suna Abubakar Bawa Ibrahim da aka fi sani da suna Habu Dogo.

    Cikin wata sanarwa da rundunar ke fitarwa a kowane mako, mai ɗauke da sa hannun, daraktan yaɗa labaran hedikwatar tsaron ƙasar, Manjo Janar Edward Buba, ya ce an kama Habu Dogo ne a ƙauyen Rumji da ke yankin ƙaramar hukumar Illela a jihar Sokoto.

    Ɗanbindigar ya kasance cikin jerin sunayen da sojojin Najeriya da Nijar ke nema ruwa a jallo, saboda yadda yake addabar yankunan ƙasashen biyu, ta hanyar kai musu hare-hare, da garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.

    Haka kuma sanarwar ta ƙara da cewa dakarunta da ke aiki a kudu maso gabashin ƙasar sun kama wasu manyan kwamandojin IPOB guda bakwai a yankin.

    Sojojin sun ce sun kama manyan kwamandojin ƙungiyar a jihohin Anambra da Imo da Abia.

    ''A tsawon kwana bakwai dakarunmu sun samu nasarar kashe 'yanbindiga 187 tare da kama 262, da kama ɓarayin mai 39, tare da kuɓutar da mutum 147 da aka yi garkuwa da su'', in ji sanarwar.

    Sojojin sun kuma ce sun samu nasarar daƙile yunƙurin satar mai a yankin kudu maso kudancin ƙasar ta aka ƙiyasta kuɗinsa da naira biliyan 1.5.

    ''Mun kuma ƙwato makamai 205 da harsasai 5,241'', kamar yadda Manjo Janar Buba ya bayyana.

  6. Gwamnatin Najeriya ta ce ta fara biyan ƙungiyar NASU da waɗanda suka yi ritaya

    Ma'aikatan ƙungiyar NASU

    Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce ta fitar da kuɗi domin biyan albashin ma'aikatan ƙungiyar ma'aikatan jami'o'in gwamnatin tarayya ta NASU da ma'aikatan ke bin gwamnati.

    Cikin wata sanarwa da ofishin Babban Akanta Janar na Ƙasar, ya fitar a Abuja, ya ce gwamnati ta fitar da kuɗin biyan ma'aitan tare da na waɗanda suka yi ritaya

    Sanarwar ta ce tuni aka fara biyan wasu daga cikin ma'aikatan ƙungiyar ta NASU.

    A makonni biyu da suka gabata ne ƙungiyar ma'aikatan jami'o'in waɗanda ba malamai ba suka sanar da shiga yajin aiki, sakamakon cigaba da riƙe musu albashi da gwamnatin ƙasar ke yi.

  7. Gwamnatin Chadi ta musanta kai hari kan fararen hula

    Mahamat Déby

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin ƙasar Chadi ta musanta kai hare-hare kan fararen hula a lokacin da sojojinta suka ƙaddamar da hare-hare kan masu iƙirarin jidadi a kusa da kan iyakar ƙasar da Najeriya.

    A ranar Alhamis ne mutanen da ke zaune a kusa da kan iyakar ƙasar da Najeriya suka ce an kashe gomman masinta bisa kuskure lokacin da wani jirgin sojin Chadi ya sakar musu bom a tsibirin da masintar ke zaune.

    Batun na zuwa ne kwanaki bayan sojojin ƙasar sun fuskanci mummunar asara cikin shekaru masu yawa da suka gabata.

    Hukumomi a N'djamena, babban birnin ƙasar sun ce sojojin ƙasar 40 ne aka kashe a makon da ya gabata, lokacin da mayaƙan Boko Haram suka kai wa sansaninsu hari makonni biyu da suka gabata.

    Shugaban ƙasar, Mahamat Déby, ya gaggauta kai ziyara yankin, tare da ƙaddamar da harin ramuwar gayya.

    Mayaƙan masu iƙirarin jihadin na iya ɓoyewa cikin mutanen gari cikin sauƙi, ba tare da gano su ba.

    Hakan ya sa sojoji ke matuƙar shan wahalar gano su, musamman sojojin sama, domin bambance su daga fararen hula.

  8. Amnesty ta nemi Shugaba Tinubu ya saki duk masu zanga-zangar tsadar rayuwa

    Tambarin Amnesty International

    Asalin hoton, AMNESTY

    Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan'Adam ta Amnesty International ta ce dole ne sukan Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya saki dukkanin waɗanda aka kama a kan zanga-zangar tsadar rayuwa.

    Da yake martani kan batun komawa shari'ar masu zanga-zangar da aka yi a wata babbar kotun tarayya jiya a Abuja, darektan ƙungiyar a Najeriya Isa Sanusi, ya ce dole ne shugaban ƙasar ya saki dukkanin waɗanda aka kama a kan zanga-zangar kuma ba tare da wani sharaɗi ba.

    Ya ce tsare mutanen tun watan Agusta saboda kawai sun yi amfani da dama da 'yancinsu na zanga-zangar lumana tare da tuhumarsu da laifuka na ban mamaki da suka haɗa da cin amanar ƙasa da ta'addanci ya nuna yadda gwamnatin Najeriya ba ta mutunta 'yancin ɗan'Adam.

    Darektan ya ce masu zanga-zangar 114 da aka gurfanar a kotun ba su yi wani abu da ya saɓa doka ba, kuma ba su cancanci irin muzgunawar da aka yi musu ba tun daga lokacin da aka kama su

    Ya ce daga cikin mutum 76 da aka fara gabatarwa a kotun a jiya, yawancinsu yara ne, kuma faɗuwar hudu daga cikinsu a kotu alama ce da ta nuna mummunan yanayin da lafiyarsu ke ciki.

    Shugaban ƙungiyar ta Amnesty ya ce tsare yara a irin wannan yanayi na tashin hankali a kan ƙin amincewarsu tare da neman mulki na gari ya nuna kudurin gwamnati na murƙushe masu suka.

  9. Hukumar UNICEF ta fara allurar rigakafin ƙyanda a wasu jihohin arewa huɗu

    Likita na allura

    Asalin hoton, UNICEF Nigeria/2016/van den Berg

    Asusun yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, ya ce zai yi wa yara aƙalla ,iliyan 3.8 allurar riga-kafin ƙyanda a wasu jihohi huɗu na arewacin Najeriya.

    Babban jami'in lafiya na hukumar ta UNICEF a Bauchi, Patrick Akor, shi ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai jiya Juma'a a Bauchi, inda ya je a yau Asabar za a fara allurar da za a yi tsawon kwana bakwai.

    Jami'in ya ce jihohin da za a yi wa yara, 'yan kusan shekara biyar zuwa shekara tara allurar su ne Adamawa da Bauchi da Gombe da kuma Filato.

    Haka kuma Mista Akor ya ce za su yi wa yara riga-kafin cutar shan-inna na ɗigawa a baki a jihohi biyar a arewacin Najeriya.

    Jihohin su ne Taraba, da Filato, da Bauchi, da Gombe, da kuma Adamawa, inda ya ce a aikin suna sa ran yi wa yara 'yan shekara biyar zuwa ƙasa har miliyan 6.8.

  10. Ƴanbindiga sun sace fasinjoji sama da asirin a jihar Niger

    Ƴanbindiga

    Asalin hoton, OTHERS

    An sace fasinjoji sama da ashirin a wasu motoci biyar a kan hanyar Mariga zuwa Kontagora da ke jihar Naija.

    Shugaban majalisar dokokin jihar wanda kuma shi ne wakilin mazaɓar Mariga inda lamarin ya faru, Abdulmalik Sarkin-Daji ya tabbatar da labarin ga manema labarai, kamar yadda jaridar Dailt Trust ta ruwaito.

    Ya ce ɓarayin sun datse hanyar ne ta Mariga zuwa Kontagora a shekaran jiya Alhamis a daidai titin Babbar-Lamba da Beri inda suka yi awon-gaba da fasinjojin.

    Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martani kan yadda sojojin Najerya suka musanta labarin da ke cewa ɓarayin daji sun kama sansanin horonsu a yankin ƙaramar hukumar Kontagora, yankin da ya kai har Mariga.

    Abdlmalik ya ce, iyalan waɗanda aka sace a baya suna kai wa ɓarayin dajin kuɗin fansa sau da dama a cikin dajin, wanda ya ce ɓangare ne na sansanin atisayen sojin.

    Ya ce wasu daga cikin waɗanda ɓarayin ke garkuwa da su sun gaya wa 'yan uwansu cewqa an tsare su ne dajin da ba shi da nisa da barikin soji na Kontagora.

    Shugaban ya ce su ma waɗanda aka sace ranar Alahamis an kai su dajin ne, inda ya yi kira ga hukumomin sojin na Najeriya da su nemi bayanai na gaskiya su je su kawar da waɗannan ɓarayin daji.

    Jariadr ta ce, kakakin rundunar 'yansandan jihar ta Naija Wasiu Abiodun ya ce zai samo cikakken bayanin satar mutanen kafin ya yi magana amma kuma ba a ji shi ba.

  11. Waɗanda suka suma a kotu, shiri ne kawai suka yi - Sufeto Janar

    IG Kayode Egbetokun

    Asalin hoton, NPF

    Babban Sufeton Ƴansan Najeriya, Kayode Egbetokun ya ce, waɗanda suka suma a kotu su shida cikin waɗanda aka kai kan zargin zanga-zangar tsadar rayuwa sun yi hakan ne da gangan domin ɗaukar hankali da ɓata sunan hukumomi.

    An gabatar da masu zanga-zangar ne su 114, jiya, Juma'a a wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, inda kafin gurfanar da su, huɗu daga cikinsu da suka hada da yara biyu suka faɗi, inda aka garzaya asibiti da su.

    Lamarin ya ɗauki hankalin duniya tare da janyo maganganu a cikin ƙasar, inda da dama ke suka a kai.

    A wata sanarwa da kakakin rundunar 'yansandan Muyiwa Adejobi ya fitar a madadin Sufet Janar ɗin, kakakin ya jadda cewa a ƙarƙashin dokokin Najeriya duk mutumin da ya kai shekarun munzalin aikta laifi, to alhakin wannan laifi da ya yi ya rataya a wuyansa ko yaya shekarunsa suke.

    Sanarwar ta ce laifukan da ake tuhumar mutanen da aikatawa sun haɗa da lalata kayan gwamnati da barazana ga tsaron ƙasa da sauransu.

    Alƙalin kotun ya bayar da belon kowannensu a kan naira miliyan goma da kuma mutum biyu masu tsaya wa kowanne.

  12. Sojojin Bolivia sun ce wata ƙungiyar 'yanbindiga ta ƙwace musu sansani

    Sansanin soji

    Asalin hoton, Reuters

    Rundunar sojan Bolivia ta ce wata ƙungiyar mai ɗauke da makamai ta karɓe iko da wani sansanin soji da ke kusa da birnin Cochabamba, sannan ta yi garkuwa da wasu sojoji.

    Ta ce kungiyar ta kuma ƙwace makamai da alburusai, kana ta buƙaci su fice nan take.

    Yankin na da ɗimbin magoya bayan tsohon shugaban ƙasar Evo Morales, wanda ya taɓa zama abokin shugaban ƙasar mai ci Luis Arce amma daga baya sun ɓata.

    Magoya bayan Mista Morales na neman a kawo ƙarshen binciken da ake yi wa tsohon shugaban ƙasar kan zargin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 16, da safarar mutane, abin da ya musanta.

  13. Gwamnatin Mali ta haramta neman jinsi ɗaya

    An riƙe hannaye

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokokin Mali ta amince da wata doka da ta haramta neman jinsi ɗaya, abun da ya sa ƙasar ta zamo ta baya-bayan nan a Afrika da ta ɗauki mataki irin wannan.

    Kafin ɗaukar wannan mataki a baya babu wata doka da ta shafi masu neman jinsi guda a Mali.

    Idan shugabannin mulkin sojin ƙasar suka rattaɓa mata hannu a dokar, duk wanda ya aikata hakan ko ma ya tallata shi zai fuskanci tuhuma a gaban kotu.

    Dukkan mambobin majalisar wucin-gadin ƙasar ne suka kaɗa ƙuri'ar amincewa da ƙudurin, in ban da mutum ɗaya.

    Kusan ƙasashen Afirka 30 sun haramta neman jinsi ɗaya, yayin da a ƙasashen Mauritania, da Somalia da Sudan aka tanadi hukuncin kisa.

  14. Kotun Ƙolin Amurka ta yi watsi da buƙatar jam'iyyar Republican kan zaɓe

    Kotun kolin Amurka

    Asalin hoton, Reuters

    Kotun ƙolin Amurka ta ba da damar ƙirga wasu dubban ƙuri'u da 'yan jam'iyyar Republican suka so ganin an yi watsi da su a jihar Pensylvania.

    Babbar kotun ta yanke hukuncin cewa masu zaɓen da suka mayar da ƙuri'un da ke da wata matsala za su iya neman a aika masu wasu, ko su kaɗa ƙuri'a a rumfunan zaɓe a ranar zaɓen gama gari.

    ‘Yan jam’iyyar Republican sun buƙaci kotun ƙolin ta dakatar da wannan hukunci, suna cewa hakan ya saba wa ƙa’idojin zaɓen jihar.

    Korar ƙarar da suka shigar a jiya, Juma'a a iya cewa wani babban naƙasu ne ga Republican ta fuskar shari'a a jihar da ake ganin ita ce za a fi kai ruwa rana a kanta.

  15. MDD da hukumomin jinƙai na duniya sun yi gargaɗi kan halin da ake ciki a Gaza

    Hari gida ya rushe

    Asalin hoton, Reuters

    Shugabanni da hukumomin jinkai na Majalisar Ɗinkin Duniya sun fitar da wani gargaɗi na haɗin gwiwa inda suka bayyana halin da ake ciki a arewacin Gaza a matsayin abin da ya wuce dukkan misali.

    Sun ce ɗaukacin al'ummar Falasdinu da ke wurin na fuskantar barazanar mutuwa daga walau dai cututtuka, ko yunwa ko tashin hankali yayin da Isra'ila ke ci gaba da kai hari babu ƙaƙƙautawa.

    Rahotanni na cewa ana ganin ƙarin yara da dangi da ke neman taimakon kusan komai ma, kuma ana ci gaba da ganin ƙaruwar waɗanda hare-haren ke shafa, ciki har da mata da ƙananan yara.

    Fatan da Amurka ta yi na ganin an tsagaita wuta ta ƴan kwanaki gabanin zaɓen ƙasar a mako mai zuwa ya ci tura, sai ma dai Isra'ila ta zafafa hare-harenta.

    A gefe guda, hukumar ta W.H.O ta ce tana fatan gudanar da wani sabon zagaye na allurar rigakafin cutar shan inna a yau Asabar.

  16. Buɗewa

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafin da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, muna muku maraba a wannan safiya ta Asabar, 02-10-2024.

    Ni Muhammad Annur Muhammad da Abdullahi Bello za mu kasance da ku daga yanzu zuwa wani lokaci a nan gaba. A yi jimirin kasancewa da mu.

    Mu fara da wannan karin maganar - Wanda ya ɗauki babban kashi ba ruwansa da gyara