Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 04/07/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Ahmad Bawage

  1. 'Ƴan Najeriya ne za su zaɓi wanda zai yi takara a ADC'

    Haɗakar ADC

    Asalin hoton, ADC

    Sabuwar haɗakar ƴan siyasa ta ADC a Najeriya ta ce ƴan ƙasar ne za su yanke hukunci kan wanda suke so ya yi wa sabuwar jam'iyyar takarar shugaban ƙasa a 2027.

    Ibrahim Hussain Abdulkarim, Jigo a sabuwar tafiyar, kuma makusanci ga Peter Obi ya ce duk wanda zai yi takarar shugaban ƙasa a sabuwar haɗakar tasu sai ƴan Najeriya ta tantace shi sun kuma amince da shi.

    ''Za a bai wa ƴan Najeriya dama su zaɓi wanda suke so, wanda suke ganin zai taimaka wa talakawa, wanda zai magance matsalar tsaro, wanda zai fitar da ƙasar daga ƙangin talauci'', in ji shi.

    Ibrahim Hussain Abdulkarim ya ce sabuwar haɗakar za ta bai wa duk wanda yake son tsayawa takara dama a fito ya bayyana wa talakawa abubuwan da zai yi musu.

    Ya ƙara da cewa cikin masalaha sabuwar tafiyar za ta raba muƙaman da ke za jam'iyyar za ta tsaya takara.

  2. Haɗakar ADC ungulu ce da kan zabo - PDP

    PDP

    Asalin hoton, PDP

    Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP ta ce ƴansiyasar da suka haɗu ƙarƙashin haɗakar ADC ungule ce da kan zaɓo.

    Kakakin jam'iyyar na ƙasa Ibrahim Abdullahi ne ya bayyana haka ranar Juma'a ta cikin shirin Ra'ayi Riga na BBC Hausa.

    Ibrahim Abdullahi ya zargi jiga-jigan PDP da ke cikin sabuwar tafiyar ADC da cewa sun shiga saboda tsantsar son rai.

    ''Sun fita daga PDP ne don wataƙila sun hango ba za a sake ba su takara ba, PDP ta bai wa wasunsu dama fiye da sau biyu, kuma ba su samu nasara ba, kuma ita PDP ai ba a yi ta domin mutum guda ba'', in ji shi.

    Kakakin na PDP ya ƙalubalanci duka mutanen PDP da ke cikin sabuwar tafiyar, da su rubuta takardar ficewarsu daga PDP a hukumance.

    Ya kuma gode wa Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Ƙasar, David Mark - wanda shi ne shugaban sabuwar hadakar - bisa matakin da ya ɗauka na rubuta takartar ficewa daga PDP.

  3. Sojojin Isra'ila sun umarci mazauna Khan Younis su fice daga yankin

    Isra’ila ta ci gaba da kai jerin hare-haren zirin Gaza, tare da umartar al’ummar wajen su gaggauta ficewa daga birnin Khan Younis da ke kudancin yankin.

    Likitoci a asibitin Nasser da ke Khan Younis sun ce dakarun Isra’ila sun kai hari da jirgin sama a wani sansani mai tantunan ƴangudun hijrah da ke yammacin birnin.

    Asibitin ya kasance guda ɗaya tilo da ya rage a waɗanda suke aiki a Gaza.

    A Yau Juma’a ne Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana shi a matsayin cibiyar kula da waɗanda da suka gamu da raunuka masu tsanani, da waɗanda aka harba a wuraren raba agaji.

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce kashi 85 cikin 100 na zirin Gaza na ƙarƙashin umarnin ficewa ko kuma yana cikin yankin da dakarun Isra’ila suka mamaye.

  4. Japan za ta fitar da shinkafa daga rumbunan gwamnatin domin karya farashinta

    Shinkafa

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Japan ta ce za ta fitar da shinkafa mai yawa daga rumbunan ajiyarta domin magance ƙarancinta a cikin ƙasar, lamarin da ya haifar da tashin farashinta a faɗin ƙasar.

    An riƙa sayar da buhun shinkafar gwamnati a farashi mai rahusa a jaɗin ƙasar, tun bayan da gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakin ciro shinkafa daga rumbunan gwamnati a watan Fabrairun da ya gabata.

    An samar da rumbunan ajiyar shinkafa a faɗin ƙasar ne domin dalilai na ko-ta-kwana ciki har da ɓarkewar annoba rashin kwayun damina.

  5. Trump ya sanya hannu kan dokar ƙara kuɗin da gwamnati ke kashewa

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya sanya hannu kan sabon ƙudirinsa dokar harajin da zai ba shi damar ƙara yawan kuɗaɗen da gwamnatinsa za ta dinga kashewa.

    An yi bikin sanya hannun ne a ofishin shugaban ƙasar, a yau Juma'a 4 ga watan Yuli, wadda ta yi daidai ramar shugaban ya sanya domin aiwatar da wasu manyan tsare-tsarensa ciki har da batun haraji da ƙara yawan kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa kan tsaro da kakkaɓe ƴancirani.

    A ranar Alhamis ne majalisar dokokin ƙasar ta amince da ƙudirin da ƴar ƙaramar rinjaye, bayan shafe kwanaki ana muhawara a kansa.

    An ɗan samu tsaiko sakamakon dogon jawabi na sa'a takwas da shugaban marasa rinjaye na jam’iyyar Democrats a majalisar, Hakeem Jeffries yayi.

    Jeffries ya ce a shirye jam'iyyarsu take ta kare ƙudirin.

    Shugaba Trump ya kira ƙudirin da mai ɗan karen ƙyau, wanda zai ƙara wa Amurka yawan bashi.

    An amince da ƙudirin duk da turjiyar da wasu daga cikin ‘yan majalisar na ɓangaren Republican suka nuna.

  6. Hukumar sanya ido kan nukiliya ta duniya ta janye jami’anta daga Iran

    Fordo

    Hukumar Kula da Nukiliya ta Duniya ta ce ta janye jami'anta da ke sanya idanu kan shirin nukiliyar Iran, yayin da rikicin kan cibiyoyin nukiliyar ƙasar ya tsananta.

    Jami'an hukumar ta IAEA ba su iya zuwa cibiyoyin nukiliyar Iran domin sanya ido ba, tun bayan hare-haren da Isra'ila da Amurka suka ƙaddamar kansu a watan da ya gabata.

    Shugaban hukumar, Rafael Grossi ya ce sanya idanu kan cibiyoyin nukiliyar Iran shi ne babban muradin hukumar a ƙasar.

    A baya-bayan nan majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri'ar yanke hulɗa da hukumar IAEA, kodayake ministan harkokin wajen ƙasar, ya ce za a ci gaba da wasu ayyukan haɗin gwiwa da hukumar.

    Hukumar IAEA ta ce har yanzu Iran ba ta sanar da ita a hukumance ba game da matakin yanke hulɗar.

  7. Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine.

    Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da amfani da makamai masu guba a yaƙin da take yi da Ukraine.

    Sun ce Rasha na amfani da hayaƙi mai sa hawaye da kuma sinadarai mai haɗari na guba, da ke sanya tari da numfashi mai wahala.

    Hukumar leƙen asirin Netherlands ta ambato hukumomin Kyiv na cewa, Rasha ta kai hare-haren makamai masu guba fiye da dubu tara (9,000) bayan mamayar Ukraine sama da shekaru uku (3) da suka gabata.

    Hukumar leƙen asirin Netherlands ta zargi Rasha da amfani da makamai masu guba domin tilasta wa sojojin Ukraine fita daga mafaka, don a fi samun sauƙin halaka su.

    Gwamnatin Netherlands ta ce irin wannan amfani da makamai masu guba barazana ne ga tsaron Turai da ma duniya baki ɗaya, kuma ba za ta amince da hakan ba.

    Sai dai Rashan ta musanta zarge-zargen.

  8. An naɗa Ahmed Musa sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

    Ahmed Musa

    Asalin hoton, Ahmed Musa/X

    Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kaptin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa a matsayin sabon shugaban gudanarwar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars.

    Cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce naɗin wani ɓangare ne ƙoƙarin ƙarfafa ƙungiyar gabanin fara sabuwar kakar Premier Najeriya.

    Dawakin Tofa ya ce an naɗa Ahmed Musa - wanda ɗan wasan ƙungiyar ne - bayan tuntuɓar masu ruwa da tsaki a harkokin wasanni a faɗin jihar.

    A watan Octoban 2024 ne Kano Pillars ta sanar da ɗaukar kyaftin ɗin na Najeriya, Ahmed Musa domin buga mata wasanni Premier Najeriya.

  9. An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

    Ƴansanda

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta kama wani tsoho mai shekara 70 bisa zargin kashe ƙanwarsa saboda rikici kan gado.

    Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Lawan Adam Shi'isu ya fitar ya ce tsohon mai suna Adamu Yakubu - ɗan asalin ƙauyen Galadanchi a yankin ƙaramar hukumar Dutse - ya samu saɓani da ƙanwarsa mai suna Hannatu Hashimu, mai shekara 45, kan rabon gadon wata gona da suka gada.

    Bayanan binciken farko da ƴansanda suka fitar, ya nuna cewa wanda ake zargin ya jefi ƙanwar tasa da sanda ne a lokacin da gardama ta yi zafi tsakaninsu kan rabon gadon.

    Gardamar - wadda ta fara da musayar kalamai - ta munana zuwa rikicin da ya kai ga bai wa hamata iska, inda wanda ake zargin ta kai wa ƙanwar tasa duka da sanda, kamar yadda bayanan ƴansanda suka nuna.

    ''Marigayiyar ta fita daga gidan a fusace, ta koma gidan aurenta, da zuwanta kuma ta faɗi ta suma, nan take aka garzaya da ita asibiti inda likitocin Babban Asibitin Dutse suka tabbatar da mutuwarta'', in ƴansandan.

    Tuni ƴansandan suka kama wanda ake zargin, inda yanzu haka suke gudanar da bincike.

  10. Mutum ɗaya ya rasa ransa bayan harin Rasha a Kyiv

    Masu aikin ceto a Ukraine sun ce mutum daya ya rasa ransa sakamakon wani gagarumin harin jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami da aka kai birnin Kyiv cikin dare.

    Shugaban hukumar kula da harkokin soja a birnin Kyiv ya ce an gano gawar ne a cikin gine-ginen da suka rushe a unguwar Svia-toshyn-skyi.

    Wannan hari na Rasha shi ne mafi girma da aka kai wa tun bayan barkewar yakin.

    Ukraine ta ce Moscow ta harba makamai da jiragen marasa matuƙa guda dari biyar da hamsin (500), inda yawancinsu suka sauka a birnin Kyiv.

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya sake kira da a kakabawa Rasha ƙarin takunkumi domin dakile barnar da take aikatawa.

    Rasha ta ce ta kai hare-haren ne kan masana’antun ƙera jirage marasa matuƙa da wasu gine-gine soji.

  11. Kenya za ta gina coci a fadar shugaban ƙasa

    William Ruto

    Asalin hoton, EPA

    Shugaban Kenya, William Ruto, ya tabbatar da cewa yana gina coci a fadar shugaban ƙasa da ke Nairobi.

    Ruto ya ce shi ne ke ɗaukar nauyin aikin, kuma babu abin da zai nemi gafara a kai.

    A baya-bayan nan ne jaridar Daily Nation ta wallafa hoton tsarin gine-ginen da ke nuna wani babban coci da tagogi masu launi da kuma wurin ibada da zai iya ɗaukar mutum dubu takwas.

    Jaridar ta ce akwai ayar tambaya ko aikin yayi daidai da kundin tsarin mulkin Kenya da ya tabbatar da ita a matsayin ƙasa mai zaman kanta daga addini.

    An kuma samu masu suka dangane da kuɗin aikin da ake hasashen zai kai dala miliyan tara, a daidai lokacin da ƴan ƙasar ke fama da tsadar rayuwa.

    Wani ɗan majalisa ya bayyana cewa Kenya ba ƙasa ce ta Kiristoci kaɗai ba, ƙasa ce da ta haɗa dukkanin addinai.

  12. Sojoji sun ce sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

    Sojojin Najeriya

    Asalin hoton, Nigerian Army/X

    Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kashe ƴanbindiga da dama a wani artabu a jihar Plateau.

    Wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar a shafinta na X, ta ce dakarunta na Operation Safe Heaven ne suka samu nasarar kashe ƴanbindigar a karamar hukumar Bokkos na jihar ta Filato.

    Sanarwar ta ce an kai samamen ne a ranar Alhamis a ƙauyukan Tutus da Hokk, da ke kan hanyar Plateau zuwa Nasarawa.

    "Sojoji sun fafata da ƴanbindigar a ƙauyen Hokk, lamarin ya kai ga mutuwar da dama daga cikinsu. Saura kuma sun tsere zuwa cikin dazuka," in ji sanarwar.

    A wani samame na daban, sojojin sun ce sun kama wani da ake zargi da safarar makamai a yankin Daffo na karamar hukumar ta Bokkos a yammacin ranar, bayan samun bayanan sirri.

    An kama mutumin ne da ake zargi yana safarar bindigogi a kan babur ɗinsa zuwa cikin daji.

    Rundunar sojin ta ce tana ci gaba da tsare mutumin da kuma makamai da suka ƙwato yayin da ake ci gaba da bincike don gano sauran waɗanda ke aikata laifin.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  13. WHO ta soki cibiyoyin rabon agaji da Amurka da Isra'ila ke mara wa baya a Gaza

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta soki cibiyoyin rabon agajin gaggawa da Amurka da Isra’ila ke mara wa baya a Zirin Gaza, inda ta ce a kawo ƙarshen abin da ta kira da kisan gilla a wuraren.

    Hukumar ta ce asibitin Nasser da ke kudancin Gaza ya rikiɗe zuwa wani babban ɗakin jinya da bayar da taimakon gaggawa, inda ake duba waɗanda suka jikkata.

    Wakilin WHO a yankin, Rik Peeperkorn, ya ce mafi yawan waɗanda aka jikkata sun kasance matasa maza da suka je cibiyoyin agaji domin karɓar abinci.

    Ya ce da an harbi da dama daga cikinsu a kai, da wuya ko ƙirji, kuma da yiwuwar wasu za su iya nakasa ta har abada.

    Tun da aka fara aiki da cibiyoyin na GHF makonni biyar da suka gabata, ofishin kare haƙƙin ɗan'adam na MDD ya tabbatar da mutuwar fiye da mutum 500 a wuraren rabon agajin.

  14. Kotu ta buƙaci majalisa ta dawo da Sanata Natasha

    Natasha

    Asalin hoton, Sanata Natasha/Facebook

    Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci majalisar dattijai ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wanda aka dakatar.

    Da take yanke hukunci, mai shari'a Binta Nyako ta kwatanta cewa dakatar da Natasha tsawon watanni shida da aka yi, ya yi tsauri.

    Kotun ta kuma ce shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio bai yi laifi ba, lokacin da ya hana Natasha yin magana a majalisa saboda lokacin ba ta zauna kan ainihin kujerar da aka ware mata ba.

    Ta kuma buƙaci Sanata Natasha ta bai wa majalisar hakuri.

    A cewar kotun, tun da ƴan majalisa suna da tsawon kwanaki 181 don zama a kowane zango, dakatar da Natasha tsawon watanni da aka yi - yana kamar hana ta aiwatar da haƙƙokinta ne ga ƴan mazaɓarta na tsawon kwanaki 180.

    Har ila yau, kotun ta ce majalisar dattawa tana da damar hukunta kowane ɗan majalisa da ya yi laifi, sai dai kada hukuncin ya yi tsaurin da zai hana aiwatar da ayyukan mazaɓar ɗan majalisa da aka dakatar.

    Mai shari'a Nyako ta kuma kori batun da Akpabio ya gabatar cewa kotun ba ta hurumin tsauraron ƙarar.

    Tun da farko, kotun ta ci Sanata Natasha tarar naira miliyan biyar saboda raina kotu, wanda ya hana ɓangarorin biyu yin magana a bainar jama'a kan batun.

    Ta kuma buƙaci Natasha ta nemi afuwa a gidajen jaridu biyu da shafinta na Facebook cikin kwanaki bakwai.

    A watan Maris ne majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Natasha bayan da ta zargi shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio da cin zarafi na lalata.

  15. Abu huɗu da suka kamata ku sani kafin fara amfani da Meta AI da ChatGPT, Rebecca Thorn, BBC 100 Women

    Meta AI da ChatGPT

    Takan taya ku yin lissafi. Za ta iya amsa tambayoyi na jarrabawar neman aiki. Za ta iya zama ma abokiyar neman shawara. Ƙirƙirarriyar Basira ta Artificial intelligence (AI) na ƙoƙarin zama komai da ruwanka.

    Fasahar na haɓaka cikin gaggawa, yayin da kamfanoni ke rige-rigen wuce juna ta hanyar fitar da sababbin tsare-tsare masu kaifin basira.

    ChatGPT na ɗaya daga cikin mafiya haɓaka a tarihi. Manhajar ta samu masu amfani da ita miliyan ɗaya kwana biyar kacal da ƙaddamar da ita, sun kai miliyan 100 bayan wata biyu, kamar yadda rahoton cibiyar International AI Safety Report ya bayyana wanda ƙasashe 30 mambobin Tarayar Turai, da Majalisar Ɗinkin Duniya, da OECD ta haɗakar tattalin arziki suka fitar.

  16. Tinubu ya miƙa ta'aziyyarsa kan rasuwar tsohon golan Super Eagles Peter Rufai

    Peter Rufai

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa ta'aziyyarsa kan rasuwar tsohon mai tsaron ragar Super Eagles, Peter Rufai.

    Ya rasu ranar Alhamis bayan shafe dogon lokaci yana jinya.

    Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar, shugaban ya nuna alhininsa kan mutuwar zaƙaran kwallon kafar, wanda masoya kwallo za su fi tunawa da "Dodonmayana".

    Peter Rufai na cikin ƴan wasan Najeriya da suka lashe gasar cin kofin Afirka a shekarar 1994 - ya mutu yana da shekara 61.

    "Zan iya tuna irin ƙoƙarin da Rufai ya yi a lokacin da Najeriya ta lashe gasar kofin Afrika a 1994 a Tunisiya," in ji Tinubu.

    Shugaban ya ce tarihin ɗan wasan zai ci gaba da wanzuwa a cikin zuƙatan ƴan Najeriya da kuma masoya kwallon kafa a faɗin duniya.

    Tinubu ya kuma roki Allah ya bai wa iyalai da kuma ƴan uwan mmacin hakurin jure rashinsa.

  17. Hare-haren Rasha cikin dare sun janyo ɓarna a birnin Kyiv

    Kyiv

    Asalin hoton, DSNS

    Bayanan hoto, Rasha ta harba makaman linzami da suka kai 550 a kan birnin Ukraine cikin dare

    Rasha ta ƙaddamar da wasu hare-haren jirage marasa matuka da na makamai masu linzami kan Kyiv, babban birnin Ukraine.

    Hukumomin Ukraine sun ce hare-haren na cikin dare sun yi ɓarna a kusan kowane lardi da ke babban birnin inda a wasu wuraren ma wuta ta tashi.

    Farmakin na zuwa ne sa'oi bayan da Shugaba Trump ya yi magana da takwaransa Vladmir Putin ta wayar tarho.

    Mista Trump ya shaida wa ƴan jarida cewa bai samu nasarar shawo kan Rasha ta tsagaita wuta ba.

    Ya ƙara da cewa har yanzu Amurka na samar wa Ukraine makamai bayan da a farkon makon nan aka dakatar da tura mata wasu makaman.

  18. Yadda rikicin cikin gida ya turnuƙe APC a Kano bayan saukar Ganduje

    Jam'iyyar APC

    Asalin hoton, APC

    Wata sabuwar dambarwa ta sake tasowa a cikin gidan jam'iyyar APC a jihar Kano, kwanaki kaɗan bayan saukar Abdullahi Umar Ganduje daga shugabancin APC na ƙasa.

    Wasu ƴaƴan jam'iyyar sun fito suna neman shugaban APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas wanda na hannun daman Ganduje ne, ya sauka daga muƙaminsa, lamarin da ɓangaren Abdullahi Abbas ke zargin jam'iyyar NNPP mai mulki a Kano da ingiza wa domin cimma wani buri nata.

    Ko da yake ba ba wannan ne karon farko da APCn ke fama da rikicin cikin gida a Kano ba, wannan karon rikicin ya ɗauki sabon salo kuma ana alaƙanta shi da saukar Ganduje daga shugabancin jam'iyyar a matakin tarayya.

  19. Giwa ta hallaka masu yawon buɗe ido biyu a Zambiya

    Giwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, An harbi giwar tare da yi mata rauni, sai dai hakan bai hana ta far wa matan biyu ba, a cewar ƴansanda

    Wata giwa ta hallaka wasu mata biyu da suka je yawon buɗe ido a ƙasar Zambiya.

    Ƴansanda sun shaida wa BBC cewa ɗaya daga cikin masu buɗe idon ta fito daga Birtaniya.

    Giwar ta far musu a gandun dajin Luangwa da ke kudancin Zambiya, kamar yadda shugaban ƴansandan yankin Robertson Mweemba ya bayyana.

    Duk ƙoƙari da masu kula da gandun dajin suka yi na ceto rayuwar masu buɗe idon ya citura.

    Dukkan matan sun mutu nan take.

    BBC ta tuntuɓi ofishin harkokin waje don jin martani.

    Mista Mweemba ya ce matan biyu suna cikin tawagar masu buɗe ido da ke zagayawa cikin gandun dajin lokacin da giwar ta afka musu a guje.

    Sun shafe kwanaki huɗu a Big Lagoon, mai nisan kilomita 600 daga Lusaka, babban birnin ƙasar - wajen da lamarin ya faru.

  20. Muna tattaunawa kan shawarar tsagaita wuta - Hamas

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, An gudanar da jana'izar Falasɗinawa da Isra'ila ta kashe a birnin Gaza

    Ƙungiyar Hamas ta ce tana tattaunawa kan shawarar tsagaita wuta da Amurka ke goyon baya da sauran ƙungiyoyin Falasɗinawa, kuma za ta gabatar da matsayarta ga masu shiga tsakani da zarar sun kammala.

    A baya dai Hamas ta ce tana neman a cimma yarjejeniyar da za ta tabbatar da kawo ƙarshen yaƙin da janyewar sojojin Isra'ila daga Gaza da kuma shigar kayan jin-ƙai zuwa yankin.

    Masu shiga tsakani sun bayar da shawarar a tsagaita wuta na tsawon wata biyu da kuma samar da hanyar kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya.

    Hakan na zuwa ne gabanin wani taro da aka shirya yi a Washington a makon gobe tsakanin Donald Trump da Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.