Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 07/12/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 07/12/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza da Ahmad Bawage

  1. 'Muna fatan 'yansiyasa su tabbatar da zaman lafiya a lokacin zaɓen Ghana'

    Goodluck Jonathan

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar raya tattalin arzikin yankin Afirka ta Yamma, Ecowas ta ce tana fatan 'yansiyasa Ghana za su tabbatar da zaman lafiya a tsawon lokacin zaɓen shugaban asar.

    Shugaban tawagar ta Ecowas - wanda shi ne tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan - ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi ga manema labarai a gundumar Ayawaso West Wuogon.

    Mista Jonathan ya ce tawagarsa za ta yi aiki da masu ruwa da tsaki wajen magance duka matsalolin da za su taso a lokacin zaɓen.

  2. Al'ummar Ghana sun nuna kishin ƙasa - Bawumia

    Ghana

    Asalin hoton, #3NewsGH/X

    Dan takarar jam'iyyar NPP a zaɓen shugaban ƙasar, Ghana Mahamudu Bawumia ya yaba da yadda zaɓen ke gudana cikin kwanciyar hankali da lumana.

    Yayin da yake jawabi ga manema labarai, jim kaɗan bayan kaɗa ƙuri'ar tasa, Mista Bawumia ya ce zaɓen na gudana yadda ya kamata ba tare da wata tangarɗa ba.

    Dan takarar na jam'iyya mai mulki ya kuma yaba da yadda al'ummar ƙasar suka fita rumfunar zaɓe tun tsakar dare, yana mai cewa hakan ya nuna yadda al'ummar Ghana ke da kishin ƙasa.

    Mista Bawumia ya kuma ce yana fatan samun nasara a wannan zaɓen, ''Nasara dai nasara ce, kuma muna fatan samun nasara da yardar Allah''.

  3. Na ji daɗin kaɗa ƙuri'ata - wadda ta yi zaɓe a karon farko

    matashiya

    Bridget Asante, wata matashiya mai shekara 25 ta kaɗa ƙuri'arta a karon farko a rayuwarta.

    Ta ce ta ji daɗin yadda ta gudanar da zaɓen a matsayinta na 'yar ƙasa, bayan da ta zaɓi ɗan takarar da take mara wa baya.

    Ms Asante ta ce tana fatan duk wanda ya lashe zaɓen zai yi ƙoƙarin gina ƙasar, da samawa matasa ayyukan yi.

    "Ina fatan wanda zai lashe zaɓen ya taimaka wajen inganta rayuwar matasan Ghana,'' in ji ta.

  4. Hanyoyi biyar da zaɓen Ghana ya yi kamanceceniya da na Amurka

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    A yau ne al'ummar Ghana ke kaɗa ƙuri'unsu domin zaɓen sabon shugaban ƙasar.

    Zaɓen na zuwa ne wata guda bayan zaɓen shugaban ƙasar Amurka da aka gudanar a farkon watan Nuwamba.

    Mutum miliyan 18 ne dai suka yi rajistar zaɓen na bana a Ghana.

    Zaɓen na Ghana na ƙunshe da wasu abubuwa da ake ganin sun yi kamanceceniya da na zaɓen shugaban ƙasar Amurka, ɗaya daga cikin ƙasashen da dimokuraɗiyya ta samu gindin zama a duniya.

    Karanta cikakken labarin a nan

  5. Mahamudu Bawumia na NPP ya kaɗa ƙuri'arsa

    Mahamudu Bawumia

    Asalin hoton, Mahamudu Bawumia

    Dan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NPP mai mulki, Mahamudu Bawumia ya kaɗa ƙuri'arsa.

    Bawumia ya kada ƙari'arsa ne a mazaɓarsa ta Walewale da ke jihar Savannah a ƙasar.

    Bawumia - wanda shi ne mataimakin shugaban ƙasar na yanzu - na fatan kafa tarihin zama Musulmi na farko da ya shugaban ƙasar.

    Mahamudu Bawumia

    Asalin hoton, Mahamudu Bawumia

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  6. Kasuwanci da harkokin yau da kullum na gudana a Accra

    Kasuwa

    Yayin da ake ci gaba da kaɗa ƙui'a domin zaɓen sabon shugaban ƙasa da 'yan majalisar dokoki a Ghana, a gefe guda kuma harkokin kasuwanci da sauran al'amuran yau da kullum na ci gaba da gudana.

    kasuwa

    Ba kamar a wasu ƙasashen na Afirka ba, a Ghana mutum zai je ya kaɗa ƙuri'a, sannan ya tafi domin gudanar da harkokinsa.

    kasuwa

    Tuni dai dama hukumar zaɓen ƙasar ta shawarci mutane su bar rumfunan zaɓe da zarar sun kammala kaɗa ƙuri'arsu.

    kasuwa

    Nan a Accra, babban birnin ƙasar harkokin kasuwanci na ci gaba da gudana yadda ya kamata.

    Kasuwa
  7. 'Muna fatan sabon shugaban ƙasar Ghana ya kawo mana guraben aiki'

    Zaɓen Ghana
    Bayanan hoto, Maryam Abubakar wata matashiya a Ghana

    Masu kaɗa ƙuri'a a Ghana na ci gaba da bayyana fatansa kan sabon shugaban ƙasar da suke zaɓa a yau.

    Wata matashiya mai suna Maryam Abubukar da BBC ta zanta da ita a wata rumfar zaɓe a birnin Accra, ta ce fatanta shi ne sabon shugaban ƙasar da za a zaɓa ya samar da guraben aikin yi ga dubban matasan ƙasar.

    ''Fatana ga sabon shugaban ƙasar da za mu zaɓa shi ne idan ya hau ya ɓullo da ayyukan yi ga matasa, duba da yadda ƙasarmu ke cikin matsin tattalin arziki '', in ji Maryam Abubakar.

    Zaɓen na zuwa ne dai a daidai lokacin da ƙasar ke fuskantar matsin tattalin arziki da tsadar rayuwa.

  8. Dan takarar mataimakin shugaban ƙasa na NPP ya kaɗa ƙuri'arsa

    Kumasi

    Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasar na jam'iyyar NPP mai mulkin ƙasar, Dakta Mathew Opoku ya kaɗa ƙuri'arsa.

    Kumasi

    Dakta Opoku ya kaɗa ƙuri'arsa a jiharsa ta Kumasi

    Kumasi
  9. Zaɓe na tafiya cikin lumana a Ghana

    masu zaɓe

    Al'ummar Ghana na ci gaba da kaɗa ƙuri'unsu cikin kwanciyar hankali da lumana domin zaɓar shugaban ƙasa da 'yan majalisar dokokin ƙasar.

    Zaɓen na bana na ɗaukar hankalai kasancewar duka mayan 'yan takara a zaɓen sun fito ne daga yankin arewacin ƙasar.

    Masu zaɓe

    Abin da ba a taɓa yi ba a tarihin Ghana tun da aka fara zaɓe a 1951 a ƙasar, a cewar Alhaji Babba Sheriff, wani mai sharhi kan al'amuran yau da kullum, kuma ɗa jarida a ƙasar.

    Mai zaɓe

    Wasu masu zaɓe da BBC ta zanta da sun ce sun fito zaɓen ne cike da fushi da fatan ceto ƙasar daga halin da ta faɗa ciki.

    ''A baya Ghana ƙasa ce da kowa ke fatan shigowa domin samun sauki, amma a yanzu mu kanmu da muke cikinta mun kasa zama ballantana baƙin da za su zo,'' a cewar wata mai kaɗa ƙuri'a.

    masu zaɓe
  10. 'Yan majalisar Koriya ta Kudu sun fara kaɗa ƙuri'ar tsige shugaban ƙasar

    Yoon Suk Yeol

    Asalin hoton, Getty Images

    Yayin da al'ummar Ghana ke kaɗa ƙuri'ar zaɓen sabon shugaban ƙasa, can kuwa a Koriya ta Kudu 'yan majalisar dkokin ƙasar ne ke kaɗa ƙuri'ar tsige shugaban ƙasar, Yoon Suk Yeol.

    Dubban mutane ne suka taru a wajen ginin majalisar dokokin suna kira a tsige shugaban ƙasar, saboda barazanar kakaba wa mutane dokoki irin na mulkin soji da shugaban ya yi a cikin wannan mako.

    Dubban masu zanga-zanga

    Asalin hoton, Getty Images

    Kalaman ba su yi wa al'ummar ƙasar da dama ciki har da 'yan majaliar daɗi ba, lamarin da ya haifar da kiraye-kirayen tsige shi.

    Sai dai Mista Yoon Suk Yeol, ya nemi afuwa daga kalaman nasa, in da ya ce ya sa kalaman nasa sun ɗaga hankula da jefa mutana a cikin damuwa.

  11. An fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasar Ghana

    Masu zaɓe

    Al'ummar Ghana sun fara kaɗa ƙuri'a a ƙoƙarinsu na zaɓar sabon shugaban ƙasar.

    Hukumar zaɓen ta ce tuni dama ta kammala shirin zaɓen, inda aka kai kayyakin zaɓe rumfunan zaɓe a kan lokaci.

    Majalisar tsaro ta yankin Ashanti ta hana jami'an tsaro na sa-kai ko na haya kusantar rumfunar zaɓe.

    Haka kuma ta haramta wa masu tsaron lafiyar manyan mutanen zuwa rumfunan zaɓe.

    Sannan ta shawarci mutane su bar rumfunar zaɓen da zarar sun kammala kaɗa ƙuri'arsa.

    masu zaɓe
  12. Yadda masu zaɓe suka fita kama layi tun da asuba

    masu zaɓe

    Masu a Ghana sun fita tun da asubahi cike da shaukin kaɗa ƙuri'unsu a zaɓen shugaban ƙasar na yau.

    Wakilan da ke wasu biranen ƙasar sun ce tun cikin dare wasu masu kaɗa ƙuri'ar suka fita domin kama layi, ta hanyar ajiye wani abu da ke alamta cewa sun kama wuri a kan layin zaɓen.

    mai zaɓe

    Cikin asubahi masu zaɓen suka riƙa fita domin kama layi a rumfunan zaɓen da za su kaɗa ƙauri'unsu

    Masu zaɓe

    Al'ummar ƙasar miliyan fiye da miliyan 18 ne dai suka yi rajistar zaɓen.

    mai zaɓe

    Wakilan BBC da suka zagaya wasu sassan ƙasar sun ce an samu fitowar mata da masata a zaɓen na yai

    masu zaɓe

    Mutum 12 ne dai ke takarar shugabancin ƙasar, sai dai ana ganin takarar za ta fi zafi ne tsakanin manyan 'yan takara biyu, Mahmudu Bawumia na NPP mai mulki, sai kuma John Mahama na NDC mai hamayya.,

    masu zaɓe
  13. Al'ummar Ghana sun hau layin zaɓe don fara kaɗa ƙuri'a

    masu zaɓe

    Al'umma ƙasar Ghana sun hau layi a rumfunan zaɓe a faɗin ƙasar domin zaɓar sabon shugaban ƙasar da zai jagorancin ƙasar nan da shekara huɗu masu zuwa.

    Shugaba Nana Akufo-Addo zai sauka bayan shafe wa'adi biyu wanda kundin tsarin mulki ya ba shi dama.

    Mataimakinsa, Mahamudu Bawumia na jam'iyyar NPP na cikin mutanen da ke takarar maye gurbinsa, inda yake fuskantar hamayya daga tsohon shugaban kasa, John Mahama na jam'iyyar NDC da ya mulkin ƙasar daga 2012 zuwa 2017.

    Al'ummar ƙasar fiye da miliyan 18 ne suka yi rajistar zaɓe a cewar hukumar zaɓen ƙasar.

    Mutum 12 ne ke fafatawar a zaɓen na yau cikin har da 'yantakarar indifenda biyu da mace guda

    Batun tattalin arziki da tsadar rayuwa ne suka dabaibaiye yaƙin neman zaɓen.

  14. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tseye barkanmu da safiyawar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki, kuma za mu fi mayar da hankali ne kan zaɓen shugaban ƙasar Ghana.

    Ku biyo a sauran shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan duka labaran da muke wallafawa.