Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya. 01/11/2024

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Ahmad Bawage da Isiyaku Muhammed

  1. Majalisar wakilan Najeriya ta yi ƙudurin ƙara kujeru domin mata da masu buƙata ta musamman

    Majalisar wakilan Najeriya ta gabatar da wani ƙudiri domin yin gyara ga sashe na 49 na kundin tsarin mulkin ƙasar na shekarar 1999.

    Ƙudurin na neman a samar da ƙarin kujeru na musamman ga mata da masu buƙata ta musamman.

    Sai dai wasu ƙungiyoyin na masu buƙata ta musamman suna ganin ba kafa dokar ba ce matsala, inda suke fargabar ko an gabatar da ƙudurin, ta kuma zama doka, da wahala ta yi ƴansiyasar ƙasar su yi amfani da ita, ko kuma a bari ta yi tasiri, har su anfama.

  2. Kamfanin BUA ya sanar da samun cinikin naira triliyan 1.07 a wata tara

    Kamfanin BUA Foods Plc ya fitar da sakamakon cinikin da ya yi a wata tara da suka gabata, wanda ya ƙare zuwa watan Satumban 2024, inda ya sanar da samun cinikin naira triliyan 1.07 a wata tara.

    Wannan na nufin samun cinikin kashi 104, wanda ƙari ne a kan naira biliyan 524.42 da kamfanin ya sanar a irin wannan lokacin a bara, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Kasuwancin sukari ne ya taimakawa kamfanin wajen samun wannan nasara, inda aka samu ƙarin cinikin kashin 73, da ƙarin cinikin kashi 160 a fulawa, da kuma ƙarin cinikin kashi 131 a taliya.

    Da yake jawabi a game da sakamakon, manajan daraktan BUA Foods, Dr Ayodele Abioye ya ce, "muna farin cikin samun wannan nasarar, wanda ke nuna yadda tsare-tsarenmu suke aiki, duk da matsalolin da harkokin kasuwanci ke ciki," in ji shi.

    Ya ƙara da cewa ciniki ya ƙaru da kashi 104, sannan riba ya ƙaru naira biliyan 333.8 ba ƙaramin nasara ba ne.

  3. Babu wahalar samun mai daga wurinmu - Matatar Dangote ga IPMAN

    Matatar Dangote ta mayar da martani ga ƙungiyar manyan dillalan man fetur, IPMAN, wadda ta ce mambobinta suna kwashe kwanaki a matatar ba tare da sun samu yin lodi ba.

    Matatar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da jami'in hulɗa da jama'anta, Anthony Chiejina ya fitar a ranar Alhamis, inda ya ƙara da cewa babu kuɗin ƴan ƙungiyar a hannunta, kamar suka bayyana.

    "Muna ƙara nanata cewa za mu iya wadatar da Najeriya da albarkatun man fetur irin su fetur ɗin da dizel da man jirgin sama da sauran su. A yanzu haka za mu iya loda tirela 2,900 a kullum, kuma muna fitar da man ta jirgin ruwa. Muna ba ƙungiyar IPMAN shawara su yi rajista da mu, kuma su fara sayan albarkatun man fetur ɗin kai-tsaye daga wajenmu domin muna da wadataccen man da suke buƙata," kamar sanarwar ta nuna.

  4. Majalisar tattalin arzikin Najeriya ta shawarci Tinubu ya dakatar da ƙudirin harajin VAT

    Majalisar ƙoli ta tattalin arzikin Najeriya NEC ta shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya janye ƙudurin yi wa harajin VAT garambawul da ya aika majalisar dokokin ƙasa domin a samu isasshen lokacin da za a tattauna tare da fahimtar juna game da abin da ake nufi gyara VAT ɗin.

    Tun da farko gwamnonin Arewa da sarakunan yankin sun yi zama na musamman a Kaduna tare da wasu masu ruwa da tsaki a yankin, inda suka yi fatali da ƙudirin na shugaban ƙasa.

    Majalisar ta bayyana hakan ne bayan zamanta na 145 a ƙarƙashin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima a Abuja.

    Majalisar ta ɗauki wannan matakin ne bayan shugaban kwamitin shugaban ƙasa na musamman kan tsare-tsare da yi wa haraji garambawul, Mista Taiwo Oyedele ya gabatar da jawabi game da tsare-tsaren da suke yi, inda majalisar ta ce akwai buƙatar a samu ƙarin lokaci domin tattaunawa tare da fahimtar juna.

    Haka kuma Kashim Shettima ya ce za su ɗauki matakai da suka dace domin tabbatar da ba a sake samun irin katsewar lantarkin da aka fuskanta ba a kwanankin baya.

  5. MDD ta yi hasashen cewa aƙalla ƙasashe 16 za su shiga matsananciyar yunwa

    Hukumomin abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya sun yi gargaɗin matsananciyar yunwa ga ƙasashe 16 a cikin watanni masu zuwa.

    Sun ce yankunan Falasɗinawa da Sudan da Sudan ta Kudu da Mali da Haiti za su fi fuskantar matsalar.

    Sauran ƙasashen da matsananciyar yunwar za ta iya ta'azzara sun haɗa da Najeriya da Chadi da Yemen da Mozambique da Myanmar da Syria da kuma Lebanon.

    Rikice-rikice ne babban abin da ke haddasa yunwar ko kuma ya ba da gudunmowa cikin halin da ƙasashen suka sa mu kansu.

  6. 'Mutum 321 suka rasu a sanadiyar ambaliya da ta shafi jihohi 34 na Najeriya'

    Majalisar ƙoli tattalin arzikin Najeriya NEC ta ce ambaliyar da ta auku a Najeriya a bana ta shafi ƙananan hukumomi 217 na jihohin Najeriya 34, inda aƙalla mutum 321 suka rasu.

    NEC ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis, inda ta ƙara da cewa ambaliyar ta shafi aƙalla mutum 1,372,557, sannan ta raba aƙalla mutum 740,743 da muhallansu.

    Gwamnan jihar Anambra, farfesa Chukwuma Soludo ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban ƙasa bayan taron na NEC, wana mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya jagoranta, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

    Ya ce ambaliyar ta jikkata mutum 2,854, ta ɓarnata gidaje 281,000, da kadada 258,000 na gonaki.

  7. Hotunan yadda ambaliya ta ɗaiɗaita yankin Valencia na Spain

  8. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'a daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu riƙa kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sadarwa domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo.

    Ku kasance tare da mu.