Labarin wasanni daga 18 zuwa 30 ga watan Janairun 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Lahadi 18 zuwa 30 ga Janairun 2026

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Mateta ya bukaci barin Crystal Palace, Crystal Palace

    Mateta

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan tawagar Faransa, Jean-Philippe Mateta ya sanar da Crystal Palace cewa yana son barin ƙungiyar, sakamakon da yake ta samun masu son zawarcinsa daga wasu ƙungiyoyin Premier League da na Turai.

    Mateta yana da yarjejeniyar watai 18 da ta rage masa a Selhurst Park, kuma a halin da ake ciki ba zai sanya hannu kan ci gaba da taka leda a ƙungiyar ba.

    Babbar ƙungiyar Italiya, Juventus tana ta ƙoƙarin ɗaukar ɗan wasan a wannan watan, amma har yanzu ba su cimma matsaya ba da Palace wadda take nukatar kusan fam miliyan 40.

    Aston Villa, wadda ta dade tana sha’awar Mateta, ita ma ta nuna sha’awar ɗaukar shi a wannan watan.

    Da yake magana a makon da ya gabata, kocin Palace Oliver Glasner ya ce suna nan suna jiran tayi mai tsoka da za a yi wa Mateta.

    Palace, wadda ta lashe FA Cup a watan Mayu, ta sayar da fitaccen ɗan wasan, Eberechi Eze ga Arsenal kan fara kakar bana, sannan kuma ta sayar da kyaftin, Marc Guehi a wannan watan Janairu, wanda ya koma Manchester City kan fam miliyan 20.

    Glasner, wanda ya sanar a makon da ya gabata cewa zai bar Palace a ƙarshen kakar bana, ya yi suka ga shugabancin Palace bayan shan kashi a hannun Sunderland ranar Asabar, inda ya ce an “yi watsi da ƙungiyar” ta hanyar tsarin ɗaukar ‘yan wasan ƙungiyar ɗin.

    Palace ta fice daga gasar FA Cup a hannun wadda da ba ta cikin manyan ƙungiyoyin Ingila, Macclesfield, a farkon wannan watan, a ɗaya daga cikin manyan abubuwan mamaki a tarihin gasar.

  2. , Daga Jaridu

    Konate

    Asalin hoton, Getty Images

    Palmeiras na zawarcin dan wasan gaban Arsenal Gabriel Jesus. Dan wasan mai shekara 28 ya murmure daga raunin da yaji na tsawon lokaci sai dai zai kasance ba shi da kwantaragi da wata kungiya a 2027 kuma watakila ya koma gida Brazil. (Mail), external

    Manchester United na bibiyar dan wasan tsakiyar Sunderland Noah Sadiki mai shekara 21, kuma watakila ta bayar da dan wasan tsakiya na kasar Uruguay, Manuel Ugarte mai shekara 24 a yarjejeniyar musaya da dan wasan Jamhuriyar Dimokraddiyar Kongo(Give Me Sport), external

    A wani labarin kuma ana sa ran Kobbie Mainoo zai ci gaba da taka leda Manchester United bayan an nada kocin rikon kwarya Michael Carrick. Dan wasan tsakiyar mai shekaru 20, wanda ya buga wa Ingila wasanni 10, na tunanin za a bada shi aro domin ya kara buga wasa akai-akai.(Fabrizio Romano), external

    Ipswich na son ta dauko dan wasa gaban Bristol City Anis Mehmeti. Dan wasan kasar Albania mai shekara zai kasance ba shi da kwantaragi da wata kungiya a bazara. (Football Insider), external

  3. Salah ya fara atisaye da Liverpool bayan kammala Afcon, Liverpool

    Salah

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool ta ci gaba da atisayen tun daga sanyin safiyar Talata inda Mohamed Salah ya koma ƙungiyar bayan buga gasar AFCON, gabanin tafiyar da za ta yi zuwa Marseille domin wasa na bakwai-bakwai a cikin rukuni a Champions League ranar Laraba.

    Salah ya taimaka wa Masar ta kare gasar AFCON a matsayi na hudu, bayan sun sha kashi da ci 1-0 a wasan kusa da na ƙarshe a hannun Senegal, wadda daga bisani ta zama zakara, sannan kuma Masar ta sha kaye a bugun fanareti a hannun Najeriya a wasan neman matsayi na uku da na huɗu.

    Liverpool na matsayi na tara a teburin Champions League da maki 12 bayan samun nasara hudu da shan kashi sau biyu.

    Marseille kuwa tana matsayi na 16 da maki uku.

  4. , Daga Jaridu

    Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Kawo yanzu Flamengo na son daukar dan wasa tsakiyar West Ham United Lucas Paqueta duk da cewa bangarorin biyu basu tuntubi juna tun makon daya gabata ba game da kula yarjejeniya da dan wasan kasar Brazil mai shekara 28. (Sky Sports), external

    Dan wasan tsakiyan Feyenoord Quinten Timber da West Ham da Aston Villa ke zawarci bai buga wa kungiyarsa tamaula ba a wasan da suka yi ranar Lahadi. Marseille ta riga ta nemi a sayar mata da dan wasan Netherlands mai shekara. (Mail), external

    Kawo yanzu Liverpool da Ibrahima Konate sun kasa cimma matsaya kan sabon kwantaragi. Dan wasan kasar Faransa, mai shekara 26, na kakarsa ta 6 a Anfield kuma ya yi ammanar cewa yana cikin masu tsaron baya da suka cancanci a biyasu albashin mai gwabi a wasannin firmiya .(Teamtalk), external

    Watakila Liverpool ta maye gurbin Konate da dan wasa mai tsaron bayan Tottenham Micky van de Ven mai shekara 24, wanda ke jan hankalin Real Madrid . (Teamtalk), external

  5. Fulham za ta ɗauki Bobb daga Manchester City, Premier League

    Fulham

    Asalin hoton, Getty Images

    Fulham na tattaunawa domin ɗaukar Oscar Bobb daga abokiyar hamayyarta a gasar Firimiya, Manchester City.

    Ɗan wasan mai shekaru 22 baya daga cikin ƴan wasan da Pep Guardiola amfani da shi a koda yaushe, sannan ƙungiyar ta sayo Antoine Semenyo daga Bournemoth a wannan watan.

    Majiyoyi sun shaida wa BBC cewa an riga an yi tattaunawa tsakanin ƙungiyoyin biyu, amma har yanzu Fulham ce ba ta gabatar da tayin sayen ɗan ƙwallon a hukumance ba.

    Bobb, wanda kuma tsohuwar ƙungiyarsa ta Bundesliga, Borussia Dortmund, ke sha’awar sake ɗaukarsa, ya buga wa City wasa 15 a wannan kakar amma bai ci ko ƙwallo daya ba.

    Karon karshe da ya buga wasa a City shi ne ranar 17 ga Disamba a karawar Carabao Cup da Brentford, inda ya fita daga wasa sakamakon rauni da ya ji tun cikin mintuna 20 na farko.

    Manchester City za ta kara da Bodo/Glimt a wasan rukuni na gasar Champions League a ranar Talata.

  6. Ƴan Real Madrid za su kara da Monaco a Champions League, Champions League

    Real Madrid

    Asalin hoton, Getty Images

    Real Madrid za ta kara da Monaco a Santiago Bernabeu a wasa na bakwai-bakwai a cikin rukuni a Champions League ranar Talata.

    Wasa na uku da za su kece raini a tsakaninsu a gasar ta Zakarun Turai, bayan da kowacce ta yi nasara ɗaya.

    Tuni Real Madrid ta bayyana ƴan wasan da za su fuskanci Monaco ranar Talata a Santiago Bernabeu.

    Ƴan wasan Real Madrid:Masu tsaron raga: Courtois, Lunin da kuma Fran González.Masu tsare baya: Carvajal, Alaba, Asencio, Fran García da kuma Huijsen.Masu buga tsakiya: Bellingham, Camavinga, Valverde, Tchouameni, Arda Güler, Ceballos, Pol Fortuny da kuma Mesonero.Masu cin ƙwallaye: Vini Jr., Mbappé, Gonzalo da kuma Mastantuono.

  7. An yi tur da halayyar wasu ƴan jaridar Morocco masu labarin wasanni, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar ƴan Jarida ta Wasanni ta Duniya (AIPS) ta yi Allah-wadai da halayen wasu daga ƴaƴanta, bayan wasan karshe mai cike da takaddama a gasar Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) da aka buga karawar karshe ranar Lahadi tsakanin Morocco da Senegal.

    A wani bidiyoyi an nuna ƴan jarida daga Morocco suna ficewa daga ɗakin taron manema labarai bayan wasan karshe, a daidai lokacin da kocin Senegal da ya yi nasara, Pape Bouna Thiaw, ya shigo ɗakin taron rike da hannun ƴarsa.

    Daga nan ne aka samu muhawara da turmutsitsi tsakanin ƴan jaridan Morocco da na Senegal, lamarin da ya yi kamari daga bisani Thiaw ya fice daga ɗakin taron.

    Senegal ta doke mai masaukin baki, Morocco da ci 1-0, amma wasan karshe ya ci karo karo da kalubale, bayan da Thiaw ya umarci ƴan wasansa da su bar fili a matsayin nuna rashin amincewa da hukuncin alkalin wasa da ya bai wa Morocco bugun fanareti.

  8. Owen zai bar Marsandi a cikin shekarar nan, Gasar Formula 1

    A Formula, babban mai tsara motocin tawagar Marsandi, John Owen, zai bar aikin a wannan shekara.

    Owen yana tare da Marsandi tun dag shekarar 2007, a lokacin da take Honda, kuma jigo ne a nasarorin da aka samu lokacin da ta lashe kofuna a karkashin sunan Brawn a 2009 da kuma Marsandi daga 2010.

  9. , Daga Jaridu

    Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Chelsea ta amince da bukatun da Jeremy Jacquet mai shekaru 20 ya gabatar mata, amma har yanzu za ta bukaci inganta yunkurinta na sayen dan wasan baya na Rennes da Faransa a tawagar 'yan kasa da shekara 21 wanda Arsenal ke so.(Metro), external

    Bournemouth za ta yi watsi da duk wani yunkurin siyan Marcos Senesi a wannan wata duk da cewa dan wasan kasar Argentina mai shekara 28 ya ki ya tsawaita kwantaraginsa da kungiyar wanda zai kare a bazara . Juventus na Barcelona duk suna sha'awar dan wasan (Talksport)

  10. Sinner ya kai zagaye na biyu a Australian Open, Australian Open

    Sinner

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴar wasan Birtaniya Katie Boulter ta sha kashi kai tsaye a hannun wadda take matsayi na goma a tennis, Belinda Bencic.

    Shi kuwa mai rike Australian Open karo biyu a jere, Jannik Sinner, ya tsallaka zuwa zagaye na gaba bayan da Hugo Gaston ya janye daga wasa a lokacin da ake cinsa 6-2, 6-1.

    Ita ma wadda ke kare kambunta, Madison Keys, ta tsallaka zagayen gaba, sai dai ƴar Birtaniya Sonay Kartal ta fice daga wasannin da ake yi a birnin Melbourne.

  11. Bournemouth ta ɗauki Toth daga Ferencvaros, Bournemouth

    Toth

    Asalin hoton, Getty Images

    Bournemouth ta sanya hannu kan sayen ɗan kasar Hungary, Alex Toth, kan fam miliyan 10.4 daga Ferencvaros.

    Yarjejeniyar ɗan wasan mai shekaru 20, wanda ya rattaba hannu kan kwantiragin shekara biyar da rabi a Bournemouth, ta ƙunshi yiwuwar ƙarin fam miliyan 2.6 kari da za bai wa ƙungiyar Hungary, tare da kashi 10 cikin 100 na idan an sayar da shi ga wata ƙungiyar.

    An kuma fahimci cewa tun a baya ƙungiyoyi irin su Benfica da Galatasaray da kuma Lazio sun nuna sha’awa sayen Toth, wanda ya buga wa kasarsa wasa tara.

    Ɗan ƙwallon ya shafe kakar 2023-24 yana buga wasannin aro a Soroksar.

    Ya fara buga wa Ferencvaros wasa a watan Disambar 2024, kuma ya buga wasa sau 52, inda ya zura kwallaye hudu.

    Toth shi ne ɗan wasa na uku da Bournemouth ta dauka kawo yanzu a watan Janairu, bayan zuwan mai tsaron raga, Fraser Forster da kuma mai tsare baya, Ade Solanke.

  12. Marseille za ta ɗauki aron Nwaneri daga Arsenal, Arsenal

    Arsenal

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Faransa, Marseille, na tattaunawa, domin ɗaukar aron ɗan wasan Arsenal, Ethan Nwaneri har zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana.

    Ana ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar, inda batun kuɗin da zai yi wasannin aro da za a biya yake daga cikin muhimman abubuwan da ake aiki a kai.

    BBC a baya ta ruwaito cewa ba a sa ran Nwaneri zai je wasannin aro wata ƙungiyar a bana, domin matashi ne mai shekara 18, zai fi samun ƙwazo da kwarewa da gogewa idan ya ci gaba da taka leda a Gunners.

    Sai dai kuma damar buga ƙwallo a wata gasar a wata ƙasar, ganin cewar baya samun buga wasa akai-akai a Gunners, wani yanayi ne da zai taimaki bunkasa sana'ar matashin ta taka leda.

    Ɗan wasan tawagar Ingila ta ƴan kasa da shekara 21 ya yi wasa 12 kacal a Arsenal a dukkan fafatawa, amma babu ko daya a gasar Firimiya, sannan ya ci kwallo daya a Carabao Cup.

    Nwaneri ya sa hannu kan sabon kwantiragi a lokacin bazara wanda zai kare a karshen kakar 2030.

  13. Rashin kokarin Real Madrid na kan dukkan ƴan wasa - Mbappe

    Real Madrid

    Asalin hoton, ge

    Kylian Mbappe ya bukaci magoya bayan Real Madrid da su daina ɗora wa Vinicius Jr laifin rashin kokarin ƙungiyar, yana mai jaddada cewa laifin ya rataya a wuyan duka ƴan wasa gabaki ɗaya.

    Ɗan ƙwallon tawagar, Faransan ya yi kiran haɗin kai gabanin wasan Real Madrid a Champions League da za ta buga a gida da Monaco ranar Talata.

    Ranar Asabar Real Madrid ta yi nasarar cin Levante 2-0 a gasar La Liga a gida - hakan ya sa saura maki ɗaya tsakaninta da Barcelona mai jan ragama, wadda ta yi rashin nasara 2-1 a gidan Real Sociedad ranar Lahadi.

    Real Madrid ta shiga ruɗani tun bayan da Barcelona ta doke ta a Saudiya ta lashe Spanish Super Cup, sannan wata karamar ƙungiya Albacete ta yi waje da Real daga Copa del Rey na bana.

    Lokacin da Real ta zo wasa da Levente ranar Asabar, sai magoya baya suka zaɓi wasu daga cikin ƴan wasa suna musu ihu har da Vinicius Jr da shi kansa shugaba, Florentino Perez.

  14. , Daga Jaridu

    Chelsea

    Asalin hoton, Getty Images

    Chelsea ta nuna wa Real Madrid cewa tana son ta sayar da ɗanwasan tsakiya na Argentina Enzo Fernandez a wannan shekarar. (Teamtalk)

    Manchester United na shirin shiga hamayya da Napoli da Atletico Madrid kan ɗanwasan tsakiya na Wolves da Portugal Joao Gomes, mai shekara 24. (Caught Offside)

    Ƴanwasan tsakiya biyu na Ingila - Ɗanwasan Nottingham Forest Elliot Anderson, mai shekara 23 da na Crystal Palace Adam Wharton, mai shekara 21 - na cikin jerin ƴanwasan da Manchester United ke farauta a wannan bazara. (Football Insider)

    Tottenham da Manchester United dukkaninsu sun tuntuɓi tsohon kocin Barcelona Xavi Hernandez. (Fichajes - in Spanish)

    Nottingham Forest na tattauna da Napoli kan aron ɗanwasan gaba na Italiya Lorenzo Lucca, mai shekara 25. (Fabrizio Romano).

  15. Djokovic ya kai zagaye na biyu a Australian Open, Australian Open

    Novak Djokovic

    Asalin hoton, Getty Images

    Novak Djokovic ya tsallaka zagaye na biyu a Australian Open a ƙoƙarinsa na lashe Grand Slam na 25 jimilla a yau din nan.

    A dai gasar a fannin mata, Iga Swiatek da Coco Gauff, sun kai zagaye na biyu cikin ruwan sanyi a wasannin da ake yi a birnin Melbourne.

    Sauran da suka kai zagayen gaba cikin salun alum sun hada da Daniil Medvedev da Alex De Minaur da Amanda Anisimova da Jessica Pegula a gaban yan kallo sama da mutum dubu 100.

  16. Van Dijk na son kara zaburar da ƴan wasan Liverpool, Liverpool

    Van Dijk

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana sa ran ƙyaftin ɗin Liverpool, Virgil van Dijk zai kira wani taron ƴan wasa na gaggawa, domin tattauna matsalolin da ke yin barazana ga burin ƙungiyar a sauran wasanin kakar bana

    Van Dijk ya nuna fushi sosai kan sakacin da suka yi da ya bai wa Burnley damar farke kwallo da ta kai sun tashi 1-1 kuma a Anfield ranar Asabar.

    Hakan ya sa ta yi kunnen doki hudu a jere a karon farko tun 2008, sannan ta kasa cin sabbin ƙungiya uku da suka hau Premier League a bana a wasan da ta yi da Leeds da Sunderland da na ranar Asabar duk a Anfield - rabonta da wannan rashin kwazon tun 1980–81.

  17. , Daga Jaridu

    Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Everton da Fulham na hamayya kan ɗanwasan gaba na Wolfsburg da Austria Patrick Wimmer, mai shekara 24. (Rudy Galetti)

    Chelsea da Manchester City na son matashin ɗanwasan gaba na Leicester City mai shekara 16 Jeremy Monga. (Fichajes - in Spanish)

    Ɗanwasan gaba na Feyenoord Anis Hadj Moussa, mai shekara 23, na cikin ƴanwasan da Chelsea ke hari amma Marseille da Benfica na sa ido kan ɗanwasan na Algeria. (Florian Plettenberg)

  18. Manchester City ta kammala ɗaukar Guehi daga Crystal Palace, Manchester City

    Mrac Guehi

    Asalin hoton, Manchester City

    Manchester City ta kammala sayen ɗan bayan tawagar Ingila, Marc Guehi, daga Crystal Palace kan kwantiragin kaka biyar da rabi, kamar City ta sanar ranar Litinin, yayin da take ƙoƙarin rage tazarar maki da ke tsakaninta da Arsenal mai jan ragamar teburin Premier League.

    City ta sayi ɗan wasan mai shekara 25 kan fam miliyan 20, wanda ya rage masa wata shida kwantiraginsa da Palace ta rage, twadda a kai kusan fam miliyan 20.

    Guehi ya zama sabon ɗan wasa na biyu da City ta saya a cikin watan Janairu.bayan Antoine Semenyo daga Bournemouth.

    Manchester City tana matsayi na biyu a teburin gasar Premier League da maki 43 daga wasa 22, inda take biye da Arsenal ta ɗaya a teburi da tazarar maki bakwai tsakani.

  19. Za a buga wasa biyu a mako na 21 a Premier ta Najeriya, Gasar Premier League ta Najeriya

    Nigerian Premier League

    Asalin hoton, NPFL

    Yau ne za a kammala wasan mako na 21 a gasar Premier ta Najeriya tsakanin Kun Khalifat da Enugu Rangers da na Warri Wolves da Katsina United.

    Sakamakon wasannin da aka buga ranar Lahadi:

    • Kano Pillars 0-1 Abia Warriors
    • Bayelsa Utd 2-0 Shooting
    • Bendel 3-2 El Kanemi
    • Enyimba 0-0 Barau FC
    • Ikorodu City 1-0 Kwara Utd
    • Nasarawa Utd 2-1 Tornadoes
    • Plateau Utd 1-0 Wikki
    • Rivers Utd 1-0 Remo
  20. City za ta ci gaba da kalubalantar cin Premier - Rodri, Manchester City

    Rodri

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasa Rodri ya sha alwashin cewa Manchester City za ta ci gaba da kalubalantar lashe Premier League zuwa karshen kakar nan, duk da shan kashi da suka yi a wasan hamayya a gidan Manchester United ranar Asabar.

    Ƙungiyar da Pep Guardiola ke jan ragama ta fara shekarar bana da tangal-tangal, inda ta tashi kunnen doki 1-1 da Sunderland da Chelsea da kuma Brighton, sannan Manchester United ta dura mata 2-0 a Old Trafford.