Teburin rukuni na uku kafin wasan Najeriya da Tunisia, Najeriya da Tunisiya

Asalin hoton, BBC Sport
Wannan shafi ne da zai ke kawo muku bayanai kan wasan Najeriya da Tunisia a gasar kofin nahiyar Afirka ta 2025 da ake yi a Moroko.
Mohammed Abdu

Asalin hoton, BBC Sport

Asalin hoton, Getty Images

Asalin hoton, ge

Asalin hoton, Getty Images
Sun fuskanci juna sau 21 jimilla, inda Najeriya ta ci wasa biyar, Tunisia ta yi nasara shida da canjaras 10, Najeriya ta ci ƙwallo 21 aka zura mata 26 a raga a tsakaninsu.
Wannan shi ne karo na bakwai da za su kara a Afcon:
Najeriya ta samu nasara uku, Tunisia tana da ɗaya da canjaras biyu, Super Eagles ta ci ƙwallo tara aka zura mata biyar a raga a tsakaninsu.
Tarihin fafatawar da suka yi a Afcon:
Ranar 16 ga watan Maris 1978, Accra
Super Eagles ce ta yi ta uku, wadda aka baiwa ƙwallo 2-0, bayan da Tunisia ta ƙi karasa wasan tun daga minti na 42 a lokacin suna 1-1.
Ranar 23 ga watan Janairun 2000, Legas wasan cikin rukuni
Ranar 11 ga watan Fabrairun 2004, Radès (Zagayen daf da karshe)
(Tunisia ta yi nasara 5–3 a bugun fenariti)
Ranar 4 ga watan Fabrairun 2006, Port Said (Zagayen kwata-fainals)
(Najeriya ta yi nasara 6–5 a bugun fenariti)
Ranar 17 ga watan Yulin 2019, Cairo (Wasan neman mataki na uku)
(Ighalo ne ya ci ƙwallon a minti na uku da take leda)
Ranar 23 ga watan Janairun 2022, Garoua (Zagayen tawaga 16)
(Msakni ne ya ci ƙwallon a minti na 47)

Asalin hoton, Getty Images
Yohan Roche ne ya zura kwallon da ta ba Benin nasara ta farko a tarihin wasannin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON), bayan ta doke Botswana da ci 1-0 a rukuni na huu a birnin Rabat ranar Asabar.
Wannan nasarar ta bai wa Benin maki uku daga wasanninsu biyu a rukuni, bayan da aka yi kunnen doki tsakanin Senegal da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo.
Benin ta ci ƙwallon a minti na 28 lokacin ta hannun Roche.
A ƙarshe Benin ta yi bikin samun nasara a gasar nahiyar ne a karon farko daga 16 da suka halarta tun bayan fara shiga Afcon a 2004, duk da cewa sun kai matakin kwata fainal a shekarar 2019.
A tarihin wasanninsu na AFCON, sunyi kunnen doki biyar tare da shan kashi karo 10.

Asalin hoton, Getty Images
Super Eagles za ta buga wasa da Tunisia a karawa ta bibiyu a rukuni na uku ranar Asabar a gasar cin kofin Afirka da ake buga wa a Morocco.
Dukkan tawagaogin biyu na fatan kaiwa zagaye na biyu a babbar gasar tamaula ta Afirka da za su kece raini a Complexe Sportif de Fes in Fes.
Super Eagles ta yi nasarar doke Tanzania 2-1, yayin da Tunisia ta ci Uganga 3-1 a wasannin farko a karawar rukuni na uku.
Shin sau nawa kasashen suka fuskanci juna a tsakaninsu?
Jama'a barkanmu da shiga shirin sharhi da bayanan wasanni kai tsaye tare da ni Mohammed Abdu Mamman Skipper Tw.
Za ku iya tafka muhawara a shirin ko bayar da gudunmuwa a BBCHausa Facebook.