Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 14/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba, 14 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Ahmad Bawage

  1. Hatsarin jirgin ƙasa a Thailand ya kashe mutum 22

    ...

    Asalin hoton, Nakhon Ratchasima provincial government

    Ƴansanda a Thailand sun tabbatar da cewa mutum 22 ne suka mutu yayin da 79 suka jikkata inda mutane takwas daga cikinsu ke cikin mawuyacin hali bayan da wata ƙatuwar ƙugiya ta aikin layin dogo ta faɗa kan wani jirgin ƙasa a arewa maso gabashin Bangkok, babban birnin ƙasar.

    Rahotanni farko sun nuna alamun cewa ana amfani da ƙugiyar ne wajen ginin gadar jirgin ƙasa mai gudun tsiya, a lokacin da ta faɗa kan jirgin.

    Hotuna da bidiyoyi da ke yawo a kafafen yaɗa labarai na ƙasar sun nuna wasu sassan taragon jirgin ƙasa na cin wuta, yayin da wasu taraguna suka kauce daga layin dogo.

    Hukumomi sun ce ana ci gaba da bincike da kuma aikin ceto, yayin da bayanai ke ci gaba da fitowa game da wannan mummunan hatsari.

  2. Trump ya gargadi gwamnatin Iran kan kashe masu zanga-zanga, Trump ya sha alwashin ɗaukar mataki mai tsauri idan Iran ta kashe masu zanga-zanga

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya sha alwashin ɗaukar mataki mai tsauri sosai kan Iran idan har ta kashe masu zanga-zangar ƙin jinin gwamnati.

    Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun ce sama da mutum 2,400 ne aka kashe a yayin murƙushe masu zanga-zangar da hukumomin Iran suka yi.

    Trump ya kuma buƙaci ƴan Iran da su ci gaba da zanga-zangar da suke yi, yana mai ba su tabbacin cewa taimakon Amurka na nan tafe.

    Ko da yake har yanzu ba a fayyace lokacin da Amurka za ta ɗauki wani mataki ba, akwai alamun cewa hakan na iya faruwa nan ba da jimawa ba.

    Shugaban na ci gaba da tattaunawa da masu ba shi shawara kan tsaro, inda ya ce yana ƙoƙarin tattara sahihan alkaluma kan yawan mutanen da aka kashe, tare da alƙawarin mayar da martani gwargwadon abin da ya tabbata.

    Sai dai ofishin jakadancin Iran a Majalisar Ɗinkin Duniya ya zargi Trump da ƙoƙarin tayar da hankula da kuma dasa harsashin hambarar da gwamnatin Musulunci ta Iran.

  3. Me ya sa Najeriya ke cin bashi duk da janye tallafin man fetur?

    ...

    Asalin hoton, Fadar shugaban Najeriya

    Har yanzu wasu ƴan Najeriya na mamaki kan dalilan da suka sanya gwamnatin ƙasar ta ci gaba da cin bashi daga waje da kuma cikin gida duk kuwa da janye tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi.

    A yayin sanar da janye tallafin man fetur da ya yi a lokacin shan rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban ƙasar, ranar 29 ga watan Mayun 2023, Shugaba Bola Tinubu ya ce za a karkatar da kuɗaɗen don gudanar da wasu muhimman ayyuka.

    Shugaba Tinubu ya koka cewa tallafin man fetur da gwamnati ke biya na janye ɗumbin dukiyar da ya kamata a yi amfani da ita wajen samar da muhimman abubuwan more rayuwa a ƙasar.

    To sai dai tun bayan hawansa mulki shekara uku da suka gabata, Shugaba Tinubu ya ci manyan basuka aƙalla takwas.

  4. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.