Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/11/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Abdullahi Bello, Isiyaku Muhammed, da Ahmad Bawage

  1. An gano maganin cutar asthma

    Asma

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu bincike a Burtaniya sun ce sun samu sabon maganin cutar asma na farko cikin shekara 50.

    Binciken ya bayyana cewa maganin, mai suna ben-ralizu-mab, ya kasance mafi tasiri kan cutar kuma ba shi da wata mummunar illa.

    Tawagar masu biniken da ke a King's College a birnin London ta bayyana maganin a matsayin babban lamari ga masu fama da cutar asma.

    Amma dai, sun yi gargaɗin cewa ana buƙatar ci gaba da gwaji a kansa, gami da tantance ko tasirinsa ya daidaita da farashinsa.

  2. Rasha ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin Ukraine

    Ukraine

    Asalin hoton, Reuters

    Ukraine ta ce a halin da ake ciki ɓangaren makamashinta na sake fuskantar wani gagarumin hari da Rasha.

    Ministan makamashi ya ce an kai hari kan cibiyoyin makamashi a faɗin ƙasar da makamai masu linzami kuma hakan ya tilasta an ɓullo da tsarin ɗauke wutar lantarki domin taƙaita ɓarnar.

    An samu rahotonin tashin bama-bamai a garuruwa da dama da suka haɗa da Odesa da Kharkiv, da kuma Lutsk.

  3. Amurka da China sun yi musayar fursunoni

    Jami’an Amurka sun ce China ta saki wasu Amurkawa uku a wata musaya da aka yi na fursunoni.

    Su ne fursunoni na karshe a China da ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta bayyana da cewa an tsare su ba bisa ƙa'ida ba.

    Wani ɗan kasuwa ɗan asalin jihar Texas mai sun Mark Swidan ana tsare da shi ne tun shekarar 2021 kan zargin fataucin miyagun ƙwayoyi.

    Yayin da sauran biyun Kai Li da John Leung aka zarge su da leƙen asiri.

    Rahotanni sun ce an sako wani babban jami'in leƙen asirin China, wanda hukumar FBI ke riƙe da shi bayan ta kama shi a wani samame da ta gudanar.

  4. Tsagaita wuta a Lebanon za ta buɗe ƙofar ta Gaza- Amurka

    Biden

    Asalin hoton, EPA

    Wakilin gwamnatin Amurka wanda ya taimaka wurin cimma yarjejeniya tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hezbollah ya ce yarjejeniyar za ta iya buɗe ƙofar kawo ƙarshen faɗa da ake yi a Gaza.

    Amos Hochstein ya shaida wa BBC cewa tsagaita wuta a Lebanon na nufin Hamas ta kasance ita kaɗai inda ba ta da wasu sauran ƙawaye.

    Ya ce, "mun yi ƙoƙari mu koyi darussan da suka dace daga gazawar yarjejeniyar da aka ƙulla a 2006 inda ba a samar da hanyoyin aiwatarwa fiye da matakan Majalisar Ɗinkin Duniya ba."

    A baya dai Ƙungiyar Hezbollah ta dage kan cewa ba za ta daina kai wa Isra'ila hari ba sai an tsagaita wuta a Gaza.

  5. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta ranar Alhamis daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu riƙa kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za kuma ku iye leƙawa shafukanmu da sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo.

    Ku kasance tare da mu.