Majalisar zartaswar Isra'ila za ta tattauna buƙatar tsagaita wuta ta kwana 60 a Lebanon

Asalin hoton, Reuters
Majalisar zartaswar ƙasar Isra'ila za ta tattauna tsagaita wuta ta kwana 60 a ƙasar Lebanon, duk da cewa a jiya Litinin ma dukkan ɓangarorin biyu sun kai wa juna hare-hare.
Tun a ranar 8 ga watan Oktoba ne ake ɓarin wuta a tsakanin Isra'ila da ƙungiyar Hezbollah, tun bayan da ƙungiyar ta Hezbollah ta harba wasu rokoki a Isra'ila.
Sai dai yaƙin ya ƙara ƙazancewa ne bayan Isra'ila ta kutsa kudancin Lebanon ta ƙasa kimanin wata biyu da suka gabata.



