Isra'ila da Lebanon sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta - Biden

Asalin hoton, US POOL
Isra'ila da Lebanon sun amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta domin kawo ƙarshen fada da ƙungiyar Hezzbollah, a cewar shugaban Amurka Joe Biden.
Da yake magana daga fadar White House, shugaba Biden ya ce yana da "albishir" kuma "ya ji dadin sanar" da cewa bayan ya yi magana da firaministocin Isra'ila da Lebanon, sun amince da yarjejeniyar.
Lokacin da yarjejeniyar ta fara aiki, Biden ya ce: "Za a kawo ƙarshen faɗan. Za a kawo ƙarshen yaƙin.
Ya sake nanata cewa nan ba da jimawa fararen hula daga ɓangarorin biyu za su samu damar komawa yankunansu cikin koshin lafiya.
Amurka, tare da Faransa da kawayenta, sun yi alƙawarin yin aiki tare da Isra'ila da Lebanon don tabbatar da "cikakkiyar" aiwatar da yarjejeniyar, in ji shi.
Ya kuma tabbatar da cewa babu wani sojan Amurka da zai shiga cikin lamarin.
Dangane da Gaza, ya ce mutanen da ke wurin ma sun cancanci a kawo karshen fadar da ake yi a yankin.



















