Isra'ila ta ce Iran ta harba mata makamai masu linzami

Asalin hoton, EPA
Isra'ila ta ce Iran ta harba mata wasu makamai masu linzami, kamar yadda rundunar sojin ƙasar ta bayyana a wata sanarwa.
Ta ce tsaron sararin samaniyarta "na ta ƙoƙari domin daƙile harin," sannan ta ba ƴanƙasar shawarar su nemi mafaka har zuwa wani ɗan lokaci.
Har yanzu dai babu cikakken bayani kan hare-haren - saboda zuwa wannan lokacin Iran ba ta tabbatar ba.
Waɗannan hare-haren na zuwa ne jim kaɗan bayan Isra'ila ta tabbatar da tsagaita wuta. Amma ama tun farko ministan harkokin wajen Iran ya ce ba su daina ɓarin wuta ba har sai Isra'ila ta daina kai mata hare-hare.

