Kotu ta ba da damar amfani da karfin soji don dakile zanga-zanga a Kenya

Asalin hoton, REUTERS
Babbar kotu a Kenya ta amince a yi amfani da karfin soji wajen maido da oda a kasar, bayan shafe kwanaki ana zanga-zangar adawa da kara haraji a kasar.
Fiye da mutum 20 rahotanni suka bayyana an kashe sakamakon zanga-zangar gama-gari da matasa suka jagoranta domin nuna adawa da tsare-tsaren gwamnati na kara haraji.
Motoci masu sulke sun yi ta shawagi a titunan Nairobi, babban birnin kasar a ranar Alhamis yayin da yan sanda suka harba hayaki mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zangar da suka yi barazanar mamaye fadar shugaban kasa.
Wani alkali ya ce jibge sojojin muhimmin mataki ne don kare gine-ginen gwamnati sai dai ya bai wa hukumomi kwanaki biyu su yi bayani kan tsawon lokacin da sojojin za su dauka suna wannan aiki da kuma bayanin irin aikin da za su yi.
"Jibge sojoji ba tare da sanin yadda aikin nasu zai kasance ba da kuma tsawon lokacin da za su dauka, yana da hadari da ka iya janyo yaki a kasar," in ji mai shari'a Lawrence Mugambi.
Kungiyar lauyoyi ta Kenya wadda ta bukaci kotun ta bai wa sojoji umarnin janyewa daga tituna, ta ce "ta martaba matsayin amma kuma ba ta yarda" da hukuncin ba.
Shugaba William Ruto a ranar Laraba ya mika wuya inda kuma ya ce zai janye kudirin da ke neman kara haraji a kasar, kwana daya bayan da masu zanga-zanga suka yi kutse a majalisar dokoki tare da cinna wuta.
Kakakin gwamnati, Isaac Mwaura, ya shaida wa BBC cewa janye kudirin babban koma-baya ne ga gwamnati saboda ta bar wani wawakeken gibi a kasafin kudi.


