Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na 10 ga watan Fabrairun 2025

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi, Ahmad Bawage da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Gwamatin Najeriya ta yi ƙarin kuɗin kafa jami'o'i

    .

    Asalin hoton, Other

    Gwamantin Najeriya ta ƙara kudin samun lasisin kafa jami'a a kasar daga naira miliyan 5 zuwa naira miliyan 25.

    Haka kuma gwamantin ta kara kudin siyen fom din kafa jami'ar daga naira miliyan ɗaya zuwa miliyan biyar.

    Shugaban hukumr kula da jami'ao'in Najeriya NUC Farfesa Abdullahi Ribadu ne dai ya sanar da hakan a wata takarda da ya fitar a ranar Litinin.

    Hukumar ta NUC ta ce matakin karin na daga cikin kokarin da suke yi na sake fasalin yadda ake kafa jami'o'in kudi a Najeriya, don ganin suna biyan bukatun yan kasar, da habaka ci gaban tsarin ilimi a banagren jami'o'in.

  2. NAFDAC ta kama kayan da aka haramta siyarwa a Aba

    .

    Asalin hoton, PIUS UTOMI EKPEI

    Hukumar kula da ingancin kayan abinci, da magunguna, da abin sha wato NAFDAC ta kai wani samame a kasuwar magungunan Ekumi da ke Aba.

    NAFDAC din ta sami nasarar kama kayan ne yayin da suka je duba magunguna da ake siyarwa ba tare da an yi musu rajista ba, da wadanda aka haramata siyar da su a kasuwa.

    Jaridar Punch ta rawaito mataimakin daraktan NAFDAC da ke yankin kudu maso kudancin ƙasar Pharmacist Omoyeni Babatunji ya shaida wa "yan jarida cewar, sun sami kaya masu yawa da aka haramta, da wadan da baa yi musu rajista ba a kasuwar.

    Haka kuma ya za su ci gaba da tantance shagunan, da ke kasuwar don tabbatar da cewar boye magunguna, da aka haranta, ko baa yi wa rajista ba, da ka iya zama illa ga lafaiyar al'umma.

  3. Yan bindiga sun YI garkuwa da wasu ma'aurata da ɗansu a Plateau

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu yan bidiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun kai hari a Unguwar Dogon Ruwa, da ke karamar hukumar Wase a jihar Fulato, inda suka yi garkuwa da wani mutum da matarsa da yaro.

    Yan bindigar dai sun kai harin ne a safiyar Litinin, inda suka raunata mutum guda a yayin da suka tafi da mutanen.

    Wasu majiyoyi sun ce lamarin ya faru da misalin karfe 11 na safe, a lokacin da mazauna yankin na tsaka da harkokinsu na yau da kullum.

    Haka kuma jaridar ta Dailytrust ta rawaito shugaba magtasan yankin Shapi’i Sambo, ya tabbatar da harin da yan bindigar suka kai, sannan ya ce yan bidngar sun yi ta harbi sama, don tsoratar da jama'a kafin daga bisani su dauki mutanen.

    Sai dai har yanzu rudunar yan sandan jihar ba ta kai, tabbatar da faruwar al'amarin.

  4. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ranatsa da sabon sakataren gwamantin Kano

    .

    Asalin hoton, facebook/Salisu Yahaya Hotoro

    Bayanan hoto, Gwamana Abba Kabir Yusuf tare da sabon sakataren gwamantin Kano

    Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ranastar da Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamantin jihar.

    An dai gudanar da rantsarwar ne a ofishin gwamanan na Kano, a wani kwarya kwaryar bikin rantsar da shi, yayin da kwamishinan shari'a na Kano Bar. Haruna Isa Dederi ya bashi rantsuwar kama aikin.

    Jaridar Dailytrust ta rawaito cewar an bashi mukamin ne bayan sauke tsohon sakatren gwamantin jihar Dr Abdullahi Baffa Bichi, da wasu kwamishinoni 5 da shugaban ma'aikatan fadar gwamanan.

    Sanarwar da mai magana da yawun gwamann na Kano Sanusu Bataure Dawakin Tofa ya fitar ta ce an zabo sabon sakataren gwamantin ne saboda kwarewar da ya ke da ita, wadda zata taimakwa wajen bunkasa manufofin da gwamantin ta Abba Kabir Yusuf ta sa a gaba.

  5. Isra'ila ta ce a shirye dakarunta suke ko da wani abu zai faru a Gaza'

    Isra'ila ta mayar da martani dangane da sanarwar da Hamas ta fitar cewa ta dakatar da sakin mutanen da take garkuwa da su .

    Wata sanarwa da ministan tsaron Isra'ila ya fitar ta ce " sanarwar dakatar da sakin waɗanda Hamas ke garkuwa da su ya saɓa yarjejeniyar tsagaita cimma wutar da ta musayar fursunoni da aka amince," in ji Israel Katz:

    "Na bai wa dakarun IDF umarnin kasancewa cikin ko-ta-kwana dangane da duk wani da ka iya biyo ba a Gaza domin kare al'umma.

    "Ba za mu bari a maimaimata abin da ya faru ranar 7 ga watan Oktoba ba.."

  6. Hamas ta dakatar da sakin ƴan Isra'ila da ta yi garkuwa da su

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Hamas

    ƙungiyar Hamas ta ce ta dakatar da sakin sauran Isra'ilawan da ke hannunta, sai yadda hali ya yi.

    Sanarwar da bangaren sojin Hamas din ya fitar ta ce "fiye da mako uku, shugabacin ƙungiyar na bibiyar yadda maƙiya suka gaza cika ka'idojin yarjejeniyar da suka cimma", a cewar Hamas din.

    "Karya wannan ƙa'ida, har da jinkirta dawowar wadanda suka rasa muhallansu zuwa arewacin Gaza, inda ake fakon su tare da harbin su, da harba musu bama-bamai, a yankuna daban-daban na Gaza, wanda hakan ke nuni da yadda suka gaza ƙyale ayyukan jinƙai, da sauran yarjejeniyar da suka cimma tunda farko.

    "Baya ga nan, dakarun na Hamas tun farko sun mutunta wannan alkawari da aka yi.

    Haka kuma sanarwa ta Hamas ta ce "sakin ƙarin wasu masu rajin kafa kasar Yahudawa a ranar Asabar, 25 ga watan 2025, sun dakatar da shi, sai nan gaba, yayin da suke jiran maƙiya, za su fara mutunta yarjejeniyar da aka cimma da aka fara aiwatarwa makkonin da suka gabata.

    "Muna sake jadada aniyarmu ta ci gaba da mutunta dukkan yarjejeniya da ka'idojin da aka gindaya, idan har masu mamayar suka bi su sau da kafa".

    An shirya sakin ƙarin wasu Isra'ilawa uku a ranar Asabar.

  7. Falasɗinawa ba su da ƴancin komawa Gaza - Trump

    Falasɗinawa

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Nan lokaci ne da dubban Falasɗinawa ke komawa gida arewacin Gaza tun bayan da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas ta fara aiki a wata da ya gabata

    Shugaba Donald Trump na Amurka ya ce shirin da yake yi a kan Gaza ya ƙunshi fitar da ɗaukacin al'ummar yankin da kuma sake gina abin da ya kira "Sake farfaɗo da Gabas Ta Tsakiya".

    Ya ce Falasɗinawa ba su da ƴancin komawa Gaza idan Amurka ta karɓi iko da yankin, kamar yadda ya shaida wa gidan talabijin na Fox a wata tattaunawa.

    Ya kuma ce za a gina wa Falasɗinawa gidaje masu kyau da inganci nesa da wajen da suke - sai dai bai faɗi takamaimen wuri ba.

    An yi watsi da shirin Trump baki-ɗaya, ciki har da ƙasashen Larabawa - wanda buƙatarsa laifi ne karkashin dokar ƙasa da ƙasa.

    Ma'aikatar harkokin waje ta Saudiyya ta ce ba za ta lamunci kutse kan ƴancin Falasɗinawa ba, yayin da ita ma Masar ta yi watsi da buƙatar.

  8. An tarwatsa iyalai sama da 8,000 a Darfur

    Darfur

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumar kula da ƙaurar jama'a ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce iyalai sama da 8,000 ne aka tarwatsa a yankin Darfur da ke arewacin Sudan, bayan wani hari da dakarun RSF suka kai.

    Mai magana da yawun wata ƙungiyar farar hula ya ce mayaƙan RSF sun far wa ƙauyen Saloma, da ke kusa da birnin El-Fasher - inda suka lalata gidaje.

    RSF ta zafafa kai hare-hare a makonnin baya-bayan nan, inda suke far wa sansanonin jama'a da kuma artabu da ƙawancen sojoji.

    Shugaban kula da ayyukan jin-kai a Sudan ya zargi dakarun RSF da toshe hanyar kai agaji - tare da saka rayukan miliyoyi a Darfur cikin barazana, inda suke faɗa da sojoji tsawon shekara biyu.

  9. An ɗora wa biri laifin ɗauke wutar lantarki a Sri Lanka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An ɗora laifin ɗaukewar wutar lantarki a faɗin Sri Lanka kan wani biri da ya yi kutse a wata tashar lantarki da ke kudancin birnin Colombo.

    Sannu a hankali dai lantarki na komawa a faɗin ƙasar mai al'umma miliyan 22, inda aka fi bai wa ɓangaren lafiya da kuma tsaftataccen ruwan sha muhimmanci.

    "Wani biri ne ya yi kutse ga babban layin ba da wutar lantarkin mu, abin da ya janyo ɗaukewar wuta," kamar yadda ministan makamashi ya shaida wa manema labarai.

    An fara samun ɗaukewar lantarkin ne da misalin karfe 11 na safe agogon ƙasar, abin da ya tilasta wa mutane da dama su koma dogaro da injunan bayar da hasken wuta.

    Jami'ai sun ce za a shafe sa'o'i kafin wuta ta koma.

    Mutane sun yi ta sukar hukumomi da kuma yin shaguɓe kan lamarin a kafafen sada zumunta.

    "Biri ɗaya ya janyo ruɗani a faɗin Sri Lanka. Lokaci ya yi ne da za a sake yin nazari kan ababen more rayuwa?", a cewar wani mai suna Mario Nawfal, kamar yadda ya rubuta a shafin X.

  10. An yi wa firaiministan Birtaniya gwajin HIV a bainar jama'a

    Keir Starmer

    Asalin hoton, EPA

    Keir Starmer ya zama Firaiministan Birtaniya na farko da aka yi wa gwajin cutar HIV a bainar jama'a, ya kuma buƙaci sauran shugabannin duniya da su ma su yi haka.

    An wallafa hotunan gwajin da aka yi masa ranar Juma'a - a matsayin wani ɓangare na kamfe ɗin tsawon mako ɗaya a Birtaniya don karfafa wa mutane su fito su yi gwajin HIV.

    Sir Keir ya ce zai fi dacewa mutane su san matsayinsu, domin samun magani.

    Gwamnatin ƙasar ta ce tana ƙoƙarin ganin an kawo karshen yaɗuwar HIV a faɗin Ingila zuwa 2030.

  11. Za a samar da ƙarin cibiyoyin buɗe-baki lokacin Ramadan a Sokoto

    ...

    Asalin hoton, Facebook/Ahmed Aliyu

    Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana cewa za ta samar da cibiyoyi na musamman ga almajirai da masu buƙata ta musamman domin yin buɗe baki a lokacin azumin Ramadan.

    Gwamnan ya bayyana haka ne a sa'ilin da ya ƙaddamar da wani sabon masallacin juma'a.

    Ya ce "mun ci alwashin faɗaɗa cibiyoyin buɗe-baki zuwa wuraren da babu su domin amfanin mabuƙata a cikin al'umma.

    Ciyarwa a lokacin azumin Ramadana wani abu ne da yawancin jihohin arewacin Najeriya ke gudanarwa a kowace shekara, sai dai batu ne da ke janyo muhawara sanadiyyar maƙudan kuɗaden da ake kashewa.

    Yayin da wasu ke kallon lamarin a matsayin tallafawa wa al'umma, wasu na ganin cewa za a iya amfani da kuɗaɗen wajen aiwatar da ayyukan gwamnati waɗanda za su amfani al'umma.

  12. Za a gudanar da zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa a Ecuador

    Zaɓen Ecuador

    Asalin hoton, Getty Images

    Za a gudanar da zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa a Ecuador a watan Afrilu bayan gaza samun wanda ya yi nasara a zagaye na farko.

    Shugaban ƙasar mai ci Daniel Noboa da abokiyar karawarsa mai sassaucin ra'ayi Luisa Gonzalez sun yi kankankan a ƙuri'un da suka samu.

    Sakamakon ya ruguza fatan da mabiya Mista Noboa ke da shi saboda sun sa ran samun sakamakon da ya fi wannan kyau.

    Duk wanda ya lashe zaɓen watan Afrilun, zai fuskanci matsi kan kawo ƙarshen rikicin da ake yi a Ecuador da magance matsalar ƙarancin ayyukan yi da kuma matslalar makamashi.

  13. An fara yi wa mutanen Indonesia gwaji kyauta don kauce wa mutuwa da wuri

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An yi wa dubban mutane gwajin lafiya kyauta a Indonesiya don kauce wa mutuwa da wuri.

    Za a yi gwajin ga ɗaukacin ƴan Indonesiya a ranar murnar bikin haihuwarsu, domin cika alkawarin da shugaba Prabowo Subianto ya yi lokacin yaƙin neman zaɓe.

    Jarirai da ƙananan yara da kuma tsofaffi na cikin waɗanda za a fara yi wa gwajin.

    A watan da ya gabata, gwamnatin mista Prabowo ta fara bai wa miliyoyin yara ƴan makaranta da kuma mata masu ciki abinci kyauta domin rage rashin abinci mai gina jiki da ke shafar yaro ɗaya cikin biyar a Indonesia.

  14. Za a rufe titi tsawon mako shida saboda kwaɗi su samu damar tsallakawa cikin aminci

    kwaɗo

    Wata ƙaramar hukuma a kudu maso yammacin Ingila ta ɗauki wani mataki da ba a saba gani ba na rufe wani titi tsawon makonni shida domin bai wa kwaɗi da dangoginsu damar tsallakawa zuwa tafkinsu na asali domin haihuwa.

    A duk shekara, motoci na kashe ɗaruruwan dabbobi kamar su kwaɗi da danginsa a kan titin da ke kusa da birnin Bath.

    Bayan ɗaukar wannan mataki, a yanzu dabbobin za su iya tsallakawa cikin aminci a tsaka da lokacin da suka fi hayayyafa.

    Adadin kwaɗin da ake da su a Birtaniya ya ragu da kashi biyu cikin uku a shekaru 30 da suka gabata saboda lalata musu muhallansu da akeyi da kuma sauyin yanayi.

    kwaɗi na tsallaka titi

    Asalin hoton, Cumberland Council

    Bayanan hoto, Alamar da ke nuna kwaɗi za su tsallaka titi
  15. Kotu ta ɗage shari'ar Nnamdi Kanu har sai yadda hali ya yi

    ...

    Babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, babban birnin Najeriya ta ɗage sauraron shari’ar da ake yi wa shugaban ƙungiyar masu rajin kafa ƙasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu.

    Ana tuhumar Kanu da laifuka da dama, waɗanda suka jiɓanci ta’addanci, tun bayan kama shi da kuma mayar da shi Najeriya a watan Yunin 2021.

    Tun a wancan lokacin ake ci gaba da tsare jagoran na IPOB, kuma duk wani yunƙuri na neman beli ya ci tura.

    A baya an samu tsaiko wajen ci gaba da shari’ar bayan da Mista Kanu ya buƙaci mai sauraron ƙarar, Binta Nyako ta tsame kanta daga shari’ar kasancewar “ba ya da ƙwarin gwiwa a kan ta.”

    Nyako ta sanar cewa ta tsame kanta daga shari’ar. To sai dai babban alƙalin kotun ya sake mayar wa alƙaliyar takardun shari’ar domin ta ci gaba da jan ragamarta, kasancewar Nnamdi Kanu bai gabatar da buƙatar tasa a rubuce ba.

    A zaman na yau Litini, mai shari’a Binta Nyako ta ce babban alƙalin kotun bai amince da janyewar tata ba.

    Ta kuma buƙaci masu kare Kanu da su gabatar da buƙatarsu a rubuce, matuƙar suna nan a kan bakarsu ta cewa sai ta tsame kanta daga shari’ar.

  16. Hanyoyin kare kai daga shan gurɓataccen ruwa

    Ruwan sha

    Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya Unicef ya ce yara miliyan 78 a Najeriya na fuskantar barazana uku da ke da alaƙa da ruwa: ƙarancin ruwa, tsaftar muhalli da tsaftar jiki.

    Cutukan da ake samu daga ruwa na faruwa ne a lokacin da kwayoyin cuta kamar bacteria da virus da kuma parasite su ka gurɓata hanyar samun ruwa saboda rashin tsafta ko zubar da bahaya ba yadda ya kamata ba ko kuma ruwa daga gonaki da ke gangarawa cikin rafi ko kogi.

    Sha ko amfani da gurɓataccen ruwa na iya janyo cutar kwalara ko typhoid ko kashin jini wanda zai kai ga amai da gudawa da rashin isasshen ruwa a jikin mutum.

    Za ku iya kare kanku da iyalanku da waɗannan matakan masu sauƙi:

    Kar ku sha ruwa sai wanda ya ke da tsafta ko wanda aka dafa; a wanke ƴaƴan itatuwa da ganyayyaki sosai kafin a ci; wanke hannu da sabulu bayan an fito daga banɗaki da kuma kafin a ci abinci; ajiye ruwa a wuri mai kyau da ke kulle, sai kuma kaucewa yin bahaya a fili.

  17. Za mu mayar da martani idan Trump ya lafta mana haraji - EU

    EU

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar Tarayyar Turai ta ce za ta mayar da martani domin kare muradun ƴan kasuwa da ma'aikata da kuma masu amfani da kayyayaki bayan shugaba Trump ya ce zai sanya harajin kashi 25 cikin dari kan ƙarafa da sanholo da ake shigarwa Amurka.

    Hukumar ta ce ba ta ga dalilin yin hakan ba, inda ta kira matakin da wanda ya saɓa doka kuma zai samar da akasin abin da ake tunani ga tattalin arziƙi.

    Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noel Barrot ya ce za su kare muradun Tarayyar Turai babu ƙaƙƙautawa.

    Ma'aikatar harkokin wajen China ta buƙaci yin tattaunawa da kuma yarjejeniya, inda ta ce ba a nasara a yaƙin kasuwanci.

    Ta buƙaci Amurka ta daina amfani da tattalin arziƙi da cinikayya a matsayin makami.

    Tun da farko China ta mayar da martani ta hanyar sanya harajin ramuwa kan kayyayakin da ake shigowa da su daga Amurka da kuɗinsu ya kai dala biliyan 14.

  18. Adadin aure da ake yi a China ya ragu

    ...

    Asalin hoton, Nanchang Railway Bureau

    Adadin aurarrakin da ake samu a China ya ragu a bara, duk da irin ƙoƙarin da hukumomi ke yi na karfafa wa mutane yin aure da kuma haihuwa.

    Adadin ya ragu da kashi biyar cikin ɗari, abin da ba a taɓa gani ba, a cewar ma'aikatar kula da lamuran al'umma.

    Haka-zalika adadin rabuwar auren da aka samu a lokacin ya ƙaru da kaɗan.

    Tsadar kula da ƴaƴa da kuma ilimi a ƙasar na daga cikin dalilan da ke janyo hakan wanda ya kai ga a bara gwamnati ta buƙaci makarantu da jam'ioi su bunƙasa nuna mahanga mai kyau kan aure da soyayya da iyali da kuma haihuwa.

    Adadin yaran da ake haihuwa a China abu ne da ke damun ƙasar ganin cewa yawan ƴan ƙasar na raguwa wasu kuma na tsufa, inda a shekaru 10 masu zuwa ake sa ran samun mutane miliyan 300 da za su yi ritaya.

  19. Gwamnatin mulkin sojin Nijar za ta yi taro don tsara komawa dimokraɗiyya

    Nijar

    Asalin hoton, AFP

    Gwamnatin mulkin soji a Jamhuriyar Nijar, ta kafa kwamitin da zai gudanar da babban taro domin tsara dokoki kan tafiyar da ƙasa a lokacin mulkinsu na rikon kwarya.

    Ɗaya daga cikin manya-manyan abubuwa da ƴan ƙasar ke son su ji shi ne wa’adin da mulkin rikon kwaryar sojojin zai ɗauka.

    "Muna tsaran duk wanda za a tura zuwa taron ya kasance wanda ya san matsalolin da suka shafi jihar da kuma zai iya cire kitse daga wuta," a cewar Abdu Ɗan Naito, shugaban ƙungiyar farar hula na Kodaye a Katsinan Maraɗi.

    Ya ce abin da ƴan ƙasar ke son gani daga wajen mambobin kwamitin shi ne a tattauna kan matsaloli da ƙasar ke ciki da kuma magance su ta yanda kowane ɗan ƙasa zai samu moriya.

    Wasu daga cikin ƴan Jamhuriyar ta Najeriyar ɗin na fatan cewa waɗanda ke cikin kwamitin ba ƴan amshin shatan sojoji da ke mulki bane.

    Taron muhawarar dai shi ne irinsa na farko da sojojin suka kira don ƙoƙarin ganin an koma mulkin dimokraɗiyya tun bayan hamɓarar da gwamnatin Mohamed Bazoum a watan Yulin 2023.

  20. Trump ya ƙara kaimi kan shirinsa na ƙwace iko da Gaza

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump na Amurka ya ƙara ƙaimi wajen shirinsa na ƙwace iko da Gaza tare da fitar da Falasɗinawa daga Zirin duk da suka da shirin nasa ke sha daga al'ummar duniya.

    Trump ya shaidawa manema labarai cewa yana son ya saya tare da mallakar Gaza domin tabbatar da cewa Hamas ba ta sake tasiri ba.

    Ya kuma bayyana cewa zai kula da Falasɗinawa tare da tabbatar da cewa sun yi rayuwa cikin aminci da kwanciyar hankali.

    Ya kuma ce yana son sauran ƙasashen Larabawa da su shiga cikin sake gina wani ɓangare na Gaza.