Isak zai ci gaba da taka leda a Newcastle United - Howe
Kociyan Newcastle United, Eddie Howe ya amince Alexander Isak ya ci gaba da hutu, kuma hakan yana kokarin ya dakushe zawarcin ɗan ƙwallon, bayan da za su buga wasan sada zumunta da Celtic.
Howe ya ce yana sa ran Isak zai ci gaba da taka leda a St James Park.
Ranar Juma'a Isak ya bar sansanin horo da suke yi a Austria, kuma ba za a je da shi Glasgow ba.
Mai shekara 25, wanda aka sauya shi a wasan sada zumunta da yake yi wa kasarsa Sweden, saboda rauni, ana ta alakanta shi da zai koma wasa Liverpool ko kuma Al-Hilal ta Saudiyya, inda Howe ke fatan riƙe Isak, wanda ya ci ƙwallo 27 a kakar da aka kammala.