Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 29/09/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 29/09/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Abdullahi Bello Diginza da Aisha Babangida

  1. Taliban ta rufe hanyoyin sadarwa a ƙasar

    Taliban

    Asalin hoton, EPA

    Mahukuntan Taliban a Afghanistan sun sanar da rufe dukkanin hanyoyin sadarwa a fadin kasar, makonni bayan da suka fara katse intanet, domin hana abin da suka bayyana a matsayin tabarbarewar tarbiyya.

    Wata kungiya mai sa ido kan harkokin yanar gizo ta ce yanzu baki ɗaya ana fama da rashin intanet a kasar. Wani jami’in Taliban ya ce rufewar za ta ci gaba har sai an bayar da wata sanarwa a nan gaba.

    Shugaban Taliban, Hibatullah Akhund-zada, ya bayar da umarnin fara cire wayoyin sadawar dake ƙarkashin kasa na intanet tun a farkon wannan wata.

    Wakilin BBC ya ce kamfanin dillancin labarai na AFP ya ce ya rasa ji ta hanyoyin sadarwa daga ofishinsa na Kabul, ciki har da ta wayar salula.

  2. Hamas ta karɓi daftarin tsare-tsaren tsagaita wuta a Gaza

    Wata majiya a Falasɗinu ta shaida wa BBC cewa jami'an Hamas sun karɓi daftarin tsare-tsaren Amurka kan tsagaita wuta a Gaza.

    Majiyar ta ce wasu wakilai masu shiga tsakani ne suka isar da saƙon daftarin zuwa ga Hamas.

    "Jami'ai daga Qatar da Masar ne suka miƙa daftarin na gwamnatin Amurka zuwa ga Hamas a Doha," in ji majiyar.

  3. Har yanzu ba mu ga tsare-tsaren Amurka na tsagaita wuta a Gaza ba - Hamas

    Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani babban jami'in ƙungiyar Hamas ya ce har yanzu ba su yi ido biyu da tsare-tsaren da Amurka ta yi ba kan tsagaita wuta a Gaza.

    Jami'in ya bayyana haka ne a zantawarsa a BBC, inda ya ce sun ji labarin tsare-tsaren na Shugaban Amurka Donald Trump, amma har yanzu ba a tura musu ba, sannan ya ƙara da cewa suna sa ran za a tura musu ne ta hannun masu shiga tsakani.

    Jami'in ya ce Hamas a shirye take ta nazarci daftarin, amma ya nanata cewa dole a kula da buƙatun ɓangaren Falasɗinu, sannan a tabbatar Isra'ila ta janye sojojinta daga Gaza domin kawo ƙarshen yaƙin.

    A game da ajiye makaman ƙungiyar, ya ce za a tattauna batun makamai ne bayan an tattauna tsare-tsaren, "Wanda ya kamata ya ƙunshi samar da ƴantancciyar ƙasar Falasɗinu."

  4. Netanyahu ya amice da tsare-tsaren Amurka na tsagaita wuta a Gaza - Trump

    Trump

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Benjamin Netanyahu ya amince da tsare-tsarensa na tsagaita wuta a Gaza.

    Trump ya ce sun samu nasarar tsara yarjejeniyar ne bayan tattaunawa tsakanin Amurka da ƙawayenta na Gabas ta Tsakiya.

    Ya ce idan an ɗabbaƙa yarjejeniyar, Isra'ila za ta janye sojojinta a hankali daga Gaza, sannan ita ma Hamas za ta saki waɗanda take garkuwa da su.

    Netanyahu ya bayyana tsare-tsaren na Trump a matsayin hanya mai kyau ta kawo ƙarshen yaƙin da ake yi a Gaza.

    Ya ce babban burin yaƙin shi ne raba Hamas da makami da ceto waɗanda ke hannun ƙungiyar daga Gaza.

    Hamas dai ta ce har yanzu ba ta samu damar ganin tsare-tsaren ba.

  5. Amurka na so ta sulhunta tsakanin Isra'ila da Iran

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yaba da yarjejeniyar Abraham Accord ta samar da zaman lafiya tsakanin ƙasashen Larabawa da Isra'ila.

    Ya ce yarjejeniyar za ta taka rawa wajen samar da zaman lafiya a Gaza ta hanyar tsagaita wutar yaƙin da Isra'ila ke yi.

    Sai dai ya ce zai yi kyau idan Iran ta shiga ciki, inda ya ce, "ina tunanin wataƙila Iran za ta shiga tsarin domin ina tunanin suna son shiga tsare-tsaren domin samar da zaman lafiya."

    Ya ce Iran za ta shiga yarjejeniyar ta Abraham, sannan ya ƙara da cewa hakan zai taimaka mata wajen haɓɓaka tattalin arzikin ƙasarta.

    Asali dai an tsara yarjejeniyar Abraham ne a shekarar 2020 domin sulhunta tsakanin ƙasashen Larabawa da Isra'ila.

  6. Netanyahu ya nemi afuwar Qatar kan hare-haren da ya kai ƙasar

    Netanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yana da yaƙinin samar da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza a ganawarsa ta yau da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.

    Masu shiga tsakani sun ce a lokacin ganawar ne Netanyahu ya kira Firaministan Qatar Mohammed bin Abdulrahman bin Jassim Al Thani daga fadar White House na gwamnatin Amurka, inda ya nemi afuwa kan hare-haren da ya ƙaddamar a ƙasar kan masu shiga tsakani na Hamas.

    Ana ganin dai wannan na cikin tsare-tsare guda 21 da Amurka ta tsara, waɗanda Netanyahu ya ce suna dubawa.

    Ana tunanin daga ciki akwai janye sojojin Isra'ila daga yankunan da ta mamaye, sannan Isra'ila ta amince da ƙasar Falasɗinu, ita kuma Hamas ta sako waɗanda take garukwa da su a cikin kwana biyu ba tare da illa ba.

  7. Shin rage wa Afirka ta Kudu maki zai ba Najeriya damar zuwa World Cup?

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Kwamitin ladabtarwa na Hukumar Ƙwallon Ƙafa FIFA ya sanar matakin da ta ɗauka a kan tawagar ƙwallon Afirka ta Kudu, inda ta rage mata maki, sannan ta ci ta tarar kuɗi.

    Kwamitin ya gano ƙasar ta yi laifi ne wajen amfani da ɗanwasan da bai kamata ya buga wasan ba, wanda tawagar da fafata da ƙasar Lesotho wato Teboho Mokoena da aka buga a ranar 21 ga watan Maris na shekarar 2025.

    FIFA ta ce amfani da ɗanwasan ya saɓa da sashe na 19 da kundin laifuka na hukumar, sannan ya kuma saɓa da sashe na 14 na kundin shirye-shiryen farko-farko na gasar cin kofin duniya na shekarar 2026.

    FIFA ta ce bayan nazarin binciken da aka gudanar, ta ƙwace nasarar da Afirka ta Kudu ta samu, sannan ta ba ƙasar Lesotho nasara a wasan.

    Haka kuma hukumar ta ci Afirka ta Kudu tarar CHF 10,000, sannan shi ma ɗanwasan, Teboho Mokoena ya samu takardar gargaɗi.

    Waɗanda aka ladabtar saboda laifukan dai suna da kwana 10 domin ɗaukaka ƙara a gaban kwamitin ɗaukaka ƙara na kwamitin ladabtarwa na Hukumar FIFA.

  8. MSF ta dakatar da ayyukanta a sassan Mozambique kan matsalar tsaro

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar agaji ta MSF, ta dakatar da ayyukanta a Mocimbowa de Praya da ke arewacin kasar Mozambique, saboda karuwar matsalar tsaro.

    MSF ta ce tashin hankalin ya hana ta damar gudanar da muhimman ayyuka kamar na gaggawa, da kula da haihuwa a wasu sassan lardin Cabul- Delgado, inda dubban mutane ke dogaro da tallafinta.

    Sojojin Mozambique sun tura karin dakarun soji, bayan jerin hare-haren ‘yan bindiga masu ikirarin jihadi sun tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu da gonakinsu.

    Tashe-tashen hankula na daɗa kamari tun bayan janyewar dakarun ƙawancen ƙasashen yankin a bara.

  9. Donald Trump zai gana da Netanyahu kan sabon daftarin yarjejeniyar Gaza

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump na Amurka zai gana da Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, a ranar Litinin a birnin Washington da misalin karfe hudu na yamma agogon birnin.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara samun ƙarin bayani kan sabon daftarin da yake yuƙurin gabatarwa domin kawo karshen yaƙin Gaza.

    Mista Netanyahu ya ce daftarin bai kammala ba tukuna, duk da cewa Shugaba Trump ya ce shugabannin ƙasashen Larabawa sun riga sun amince da shi.

    Wakiliyar BBC ta ce shirin bai tanadi tursasawa Falasɗinawa barin Gaza ba, amma ya buƙaci a gaggauta sakin fursunonin Isra’ila ta hanyar musaya da na Falasɗinu.

    A ranar Juma’a da ta gabata ne, Mr Netanyahu ya shaida wa zauren babban taron Majalisar Dinkin Duniya cewa, Isra’ila za ta ci gaba da yaƙar Hamas.

  10. Maldova na samun nasara a ƙoƙarinta na shiga Tarayyar Turai - Maya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugabar Moldova, Maya Sandu, ta ce nasarar da jam’iyyarta mai goyon bayan shiga Tarayyar Turai ta samu a zaben majalisar dokokin ƙasar, na nuna cewa ‘yan ƙasar sun san yadda za su haɗa kansu idan makomar ƙasar ta shiga cikin haɗari.

    Ms Sandu ta bayyana wannan nasara a matsayin babban cigaba ga burin Moldova na shiga Tarayyar Turai.

    Shugabannin Turai sun taya ƙasar murnar sakamakon, suna masu cewa hakan hujja ce ta jajircewar Moldova ga dimokradiyya.

    Shugaban Ukrain Volodmire Zalensky ya ce dole su daƙile ƙarfin Ikon Rasha wajen hana ƴaduwa zuwa yankin Turai, kuma dole ne mu hada kai tare da taimawaka Moldova.

  11. An tura sojoji don ƙashe wutar daji a Namibiya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin ƙasar Namibia ta tura sojoji 500 domin taimakawa wajen yaƙi da gobarar da ta ƙona kashi ɗaya bisa uku na babban Gandun Daji na Etosha, daya daga cikin manyan wuraren ajiyar dabbobi a Afirka, in ji jami’ai.

    Wannan gandun daji da ke arewacin ƙasar, wadda mafi yawan ta hamada ce, na ɗauke da nau’ikan dabbobi 114 kuma yana ɗaya daga cikin manyan wuraren yawon buɗe ido.

    Gobarar ta fara ne a ranar 22 ga Satumba kuma ta yaɗu cikin sauri saboda iska mai karfi da kuma busassun ciyayi.

    Lamarin ya haifar da babbar illa ga muhalli, in ji ma’aikatar muhalli da fadar shugaban kasar.

  12. 'Sojojin Myanmar sun mayar da ƙauyukan Musulmin Rohingya sansaninsu'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani bincike da ya samu goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce an samu ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa sojojin ƙasar Myanmar sun maida kauyukan musulmi yan kabilar Rohingya da gidajensu da suka lalata a jihar Rakhine wuraren gudanar da ayukan soji

    Musulmi ƴan ƙabilar Rohinja waɗanda ba su da rinjaye fiye da miliyan ɗaya ne suka tsere daga harin da aka kai a shekarar 2017 kuma har yanzu suna zaune a sansanoni masu fama da cunkuso a makwabciya Bangladesh.Rahoton ya ce an gina sansanin soji a wuraren da suka rage a kauyukan jihar Rakhine,bayan abin da Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana matakin daki-daki kan share wata kabila daga ban kasa.

    An gina sabbin hanyoyi da gine-gine an kuma yi filin tashi da saukar jirgi mai sauka ungulu a inda aka rusa gidaje,da rusa wuraren tarihi.

    Rahoton ya kuma ce ya tattara bayanai daga shaidu, da hotunan tauraron dan adam, da bidiyo da kuma bayanan da jami'ai suka bayyana.

    Kawo yanzu gwamnatin sojin Myanmar ba ta maida martani kan wannan rahoton ba.

  13. Me ya sa ake zargin cewa ana yin kisan-ƙare dangi a Najeriya?

    ...

    Asalin hoton, Fadar shugaban Najeriya

    Gwamnatin Najeriya ta yi kakkausan Allah wadai da nesanta kanta da wasu rahotonnin da ke cewa ƴanbindiga na aikata kisan ƙare-dangi a ƙasar.

    Wasu kafofin yaɗa labaran intanet na ƙasashen waje da fitattun masu amfani da shafukan sada zumunta ne suka yi ta yaɗa zargin cewa ƴanbinga a ƙasar na yin wani tsari da suke aikata kisan ƙare-dangi kan mabiya addinin Kirista a ƙasar.

    Cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar, ma'aikatar yaɗa labaran ƙasar, ta ce, zarge-zargen ba su da tushe balle makama, kuma an ƙirƙire su ne domin raba kan al'ummar ƙasar.

  14. Ma'aikatan PENGASSAN sun rufe wasu manyan ma'aikatun mai na gwamnati

  15. Mahara suka kashe ƴan bijilanti 10 a Kwara

  16. Amurka na son Hamas ta miƙa wuya domin a tsagaita wuta a Gaza

  17. Gwamnatin Najeriya ta shiga tsakani a rikici Dangote da PENGASSAN

  18. Ana taron nema wa Arewacin Najeriya 'mafita' a Abuja

  19. Mummunan tasirin da rikicin matatar Dangote da PENGASSAN zai yi a Najeriya