Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 17/01/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Isiyaku Muhammed da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Donald Trump ya fitar da sabon hotonsa na Shugaban ƙasa

    Hoton zababben shugaban Amurka da za a rantsar ranar Litinin, Donald Trump

    Asalin hoton, TRUMP VANCE TRANSITION TEAM HANDOUT/EPA

    Bayanan hoto, Hoton zababben shugaban Amurka da za a rantsar ranar Litinin, Donald Trump

    A hukumance an bayyana hotuna sabon shugaban Amurka, Donald Trump da mataimakinsa, JD Vance gabanin rantsar da su a ranar Litinin mai zuwa.

    Dukkanin mutanen biyu suna sanye ne da rigar kwat mai launin shuɗi, da farar riga a ciki, sai kuma shuɗin lakatayi.

    Zaɓaɓɓen mataimakin shugaban Amurka, JD Vance

    Asalin hoton, TRUMP VANCE TRANSITION TEAM HANDOUT/EPA

    Bayanan hoto, Zaɓaɓɓen mataimakin shugaban Amurka, JD Vance

    Yanayin fuskar Trump a hoton ya yi hannun riga da na mataimakinsa, JD Vance, inda Trump ya murtuke fuska tare da tsuke baki.

    Shi kuwa JD Vance ya saki fuska tare da yin murmushi, sannan ya rungume hannu a hoton nasa.

    Hoton Trump na wannan karo ya sha bamban da wanda ya yi amfani da shi a mulkinsa na farko a shekarar 2017.

    Hoton da Donald Trump ya yi amfani da shi a wa'adin mulkinsa na farko a 2017

    Asalin hoton, Library of Congress

    Bayanan hoto, Hoton da Donald Trump ya yi amfani da shi a wa'adin mulkinsa na farko a 2017

    Duk da cewa a hotonsa na baya yana sanye ne da kaya shigen irin na yanzu a hoton, to amma an ga yadda ya yi murmushi a cikin hoton.

  2. Tsananin sanyi ya sa za a yi bikin rantsar da Trump a cikin ɗaki

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Donald Trump

    Za a mayar da bikin rantsar da Donald Trump a matsayin shugaban Amurka - wanda za a yi a ranar Litinin - zuwa cikin wani ɗakin taro.

    An kwashe makonni ana shirya yadda za a yi bikin a farfajiyar Majalisar Dokokin Amurka ta Capitol da ke birnin Washington, sai dai a yanzu an yanke shawarar yin bikin a ƙarƙashin gubbar Majalisar.

    Wannan sauyi na nufin mutane ƙalilan ne za su samu halartar wurin rantsuwar.

    Sai dai Donald Trump ya ce za a haska kai-tsaye yadda rantsuwar za ta gudana a wani katafaren ɗakin taro da ke maƙwaftaka da majalisar.

    Ronald Reagan ne shugaban ƙasa na ƙarshe da aka yi bikin rantsar da shi a cikin ɗakin taro, lokacin da ya sha rantsuwar wa'adin mulkinsa na biyu, a shekarar 1985.

  3. Za mu iya sassauto da farashin kaya a shekarar nan - Gwamnatin Tinubu

    Wale Edun

    Ministan kuɗi na Najeriya, Wale Edun, ya buƙaci ƴan kasar su bai wa gwamnati lokaci, kasancewar tsadar rayuwa da ake fama da shi a ƙasar zai sauko nan ba da dadewa ba.

    A hirarsa da BBC, Mista Edun ya ce ya yi amannar cewa hauhawar farashin kayayyaki da a yanzu ta kai kashi 35% za ta ragu da rabi cikin shekarar nan.

    Ya alaƙanta matsalar tattalin arziƙin da ƙasar ke fuskanta kan gyare-gyaren harkokin kuɗi da gwamnati ta yi a baya-bayan nan, sai dai ya yi imanin cewa ƴan ƙasar za su ga amfanin hakan nan ba da jimawa ba.

    Ƙwararru a fannin tattalin arziƙi sun alaƙanta hauhawar farashin kayyyakin kan karyewar darajar ƙudin ƙasar, da cire tallafin man fetir da kuma matuƙar buƙatar kayyayaki a lokacin bukukuwan ƙarshen shekara.

  4. Tinubu ya yaba wa gwamnonin Najeriya bisa amincewa da ƙudurin haraji

    Bola Ahmed Tinubu

    Asalin hoton, Tinubu Facebook

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa ƙungiyar gwamnonin Najeriya saboda amincewar da suka yi da ƙudurin yin gyara ga dokar haraji, wanda a yanzu ke gaban majalisar dokokin tarayya, domin neman amincewa.

    Cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan yaɗa labarai da tsare tsare, Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya jinjina wa gwamnonin kan sadaukarwarsu, wadda za ta samar da haɗin kai tsakanin shugabanni a faɗin ƙasar, ba tare da la'akari da ɓangaranci ko ƙabilanci ko kuma na siyasa ba.

    Tinubu ya bayyana cewa babbar manufar sabon ƙudurin dokar harajin ita ce "taimaka wa talaka, da bunƙasa gasa a fannin tattalin arziƙi, da kuma janyo hankalin masu zuba jari na cikin gida da kuma ƙasashen waje.

    A cikin sanarwar, Tinubu ya ce sabunta dokar harajin ƙasar, wadda tuni aka daina yayin ta abu ne mai muhimmanci.

    A ranar Alhamis ne gwamnonin Najeriya suka amince da ƙudurin dokar harajin bayan sun yi mata wasu ƴan gyare-gyare.

    Dokar, wadda shugaba Tinubu ya gabatar wa Majalisar Dokokin Najeriya ta haifar da zazzafar muhawara, lamarin da ya kai ga jinkirin amincewa da ita.

    Tun farko, gwamnoni da dattaijan yankin arewacin ƙasar sun yi watsi da ƙudurin, inda suka bayyana shi a matsayin wanda zai cutar da al'umma.

    Daga baya shugaban ƙasar ya buƙaci ma'aikatar shari'a ta ƙasar ta yi aiki tare da Majalisar Dokoki domin warware matsalolin da suka janyo cece-ku-ce a kan dokar.

    Yanzu dai Tinubu ya buƙaci majalisar dokokin tarayya ƙasar ta hanzarta tattaunwa kan ƙudirin harajin domin amincewa da shi.

  5. Kotun ƙolin Amurka ta amince da haramta amfani da TikTok

    TikTok

    Asalin hoton, Getty Images

    Kotun ƙoli ta Amurka ta tabbatar da dokar haramta amfani da manhajar TikTok a ƙasar, sai dai idan kamfanin da ya mallaki manhajar, wato ByteDance, ya amince ya sayar da manhajar kafin 19 ga watan Janairu.

    Kamfanin ByteDance, na China, ya ƙalubalanci dokar kuma ya musanta cewa yana saɓa dokar kare ƴancin tofa albarkacin baki kan masu amfani da manhajar su fiye da miliyan 170 a Amurka.

    Sai dai Kotun ƙolin ya yi watsi da ƙalubalantar hukuncin da kamfanin ya yi, wanda hakan ke nufin wajibi ne manhajar TikTok ɗin ta samu mai sayenta da aka amince da shi domin samar da manhajar samfurin Amurka ko kuma ta fuskanci dakatarwa.

    Hukumomi a Amurka da ƴan majalisu sun zargi kamfanin ByteDance da alaƙa da gwamnatin China kuma sun bayyana manhajar a matsayin barazana ga tsaron ƙasar.

  6. Majalisar tsaron Isra'ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

    Netanyahu

    Asalin hoton, Getty Images

    A wani cigaba a game da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, majalisar tsaron Isra'ila ta amince da yarjejeniyar.

    Ofishin Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ne ya sanar da hakan, inda wata sanarwa da suka fitar ta ce, majalisar ta bayar da shawarar amincewa da yunƙurin gwamnati na shiga yarjejeniyar tsagaita wutan.

    Tun da farko, rahotanni sun ce yarjejeniyar ba za ta kammala ba, har sai majalisar ta amice da batun.

    An gudanar da zaman tattaunawar ne yau, wanda ya ɗauki tsawon awowi ana yi.

  7. Matatar Dangote ta ƙara farashin man fetur zuwa naira 955

    Dangote

    Asalin hoton, Getty Images

    Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙara farashin man fetur zuwa naira 955.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma'a kan ƙara farashin man, inda matatar ta ce za ta riƙa sayar da kowace lita a kan farashin naira 955 ga kwastomomin da za su saya tsakanin lita miliyan biyu zuwa lita miliyan 4.99.

    Sai dai sanarwa ta ce masu sayan fetur ɗin da yawa daga lita miliyan zuwa sama, za su riƙa saya ne a kan naira 950, kamar yadda Daily Trsut ta ruwaito.

  8. Iran da Rasha za su ƙulla yarjejeniyar tsaro ta shekara 20

    Rasha

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya isa birnin Moscow domin ganawa da Shugaban Ƙasar Rasha, Putin.

    Ana sa ran shugabannin biyu za su gana ne tare da sa hannu a yarjejeniyar haɗin gwiwa kan harkokin tsaro da kimiyya da fasaha da makamashi da kasuwanci na shekara 20.

    Rasha na da alaƙa mai kyau da Iran da China da Koriya ta Arewa, tun bayan da far wa Ukraine da yaƙi, inda rahotanni suka nuna ta yi amfani da jirage marasa matuƙa na Iran.

    Ƙasashen yamma sun zargi Iran da ba Rasha makamai, ciki har da makamai masu linzami, kuma suna nuna damuwa kan haɗakar ƙasashen biyu.

    Ƙasashen biyu dai suna fama da takunkumi daga ƙasashen yamma.

  9. Tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka a 2025 zuwa 2026 - Bankin Duniya

    Bankin duniya

    Asalin hoton, Getty Images

    Bankin Duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka da aƙalla kashi 3.6 a tsakanin shekarar 2025 zuwa 2026.

    Bankin ya bayyana haka ne a rahotonsa na hasashen tattalin arzikin duniya na 2025 da ya fitar a ranar Alhamis, 17 ga watan Janairu mai taken Global Economic Prospects January 2025.

    "Tattalin arzikin yankin hamadar Afirka zai haɓaka da kashi 4.1 a shekarar 2025, da kuma kashi 4.3 a shekarar 2026,"

    Rahoton ya ƙara da cewa, "a Najeriya kuma, ana hasashen tattalin arzikin ƙasar zai haɓaka da aƙalla kashi 3.6 a tsakanin shekarar 2025-26. Ana kuma hasashen hauhawar farashin kayayyaki zai ragu," kamar yadda tashar Channels ta ruwaito daga rahoton.

    Haka kuma rahoton ya ƙara da cewa man fetur da ƙasar ke samarwa zai ƙaru a tsakankanin lokacin da ake hasashen haɓakar tattalin arzikin ƙasar, amma duk da haka ba zai kai asalin abin da OPEC ta yi hasashen ƙasar za ta riƙa samarwa ba.

  10. Ƴanbindiga sun kashe sojoji 14 a Burkina Faso

    Burkina Faso

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu ƴanbindiga masu ikirarin jihadi sun kashe jami'an tsaron Burkina Faso a arewa maso gabashin ƙasar.

    Mayaƙan sun kai harin ne a kan jerin gwanon motocin fararen hula da suka samu rakiyar sojoji da misalin ƙarfe huɗu na yamma a ranar 11 ga Janairu, kamar yadda rediyon RFI ya ruwaito.

    Jami'an tsaron na raka matafiya ne da suka taso daga garin Dori da ke yankin Seytenga zuwa gabashin ƙasar da ke maƙwabtaka da Nijar.

    "Mayaƙan sun kai harin ne kan motocin, inda jami'an tsaron ƙasar da ake kira da genarmerie guda huɗu da sojoji 14 suka rasu, kuma aƙalla fararen hula uku, ciki har da mutum biyu ƴan Jamhuriyar Nijar suka rasu."

    Haka kuma aƙalla mutum 14 ne suka ɓace, kuma ana cigaba da nemansu.

    Rediyon ya ƙara da cewa bayan kashe jami'an tsaron, mayaƙan sun kwashe makamai, sannan suka ƙona wasu.

  11. Ya kamata mu haɗu domin shirya tsakanin Kwankwaso da Ganduje ­— Kofa

    Kwankwaso da Ganduje

    Asalin hoton, RABIU MUSA KWANKWASO/SM

    Shugaban kwamitin gidaje na majalisar wakilai ta Najeriya, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a Kano da su haɗa ƙarfi da ƙarfe domin shiga tsakani har a samu maslaha tsakanin tsofaffin gwamnonin jihar Kano, Rabiu Musa Kwanwaso da Abdullahi Umar Ganduje.

    Kofa ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da ya yi da wani gidan rediyo, inda ya ce rikicin da ke tsakanin manyan jagororin siyasar jihar bai dace ba, kuma jihar ce take shan wahala.

    Ya ce dukkan biyun sun samu dukkan nasarorin da ake buƙata a rayuwa, "kuma ba kowa ba ne Allah yake ba irin waɗannan nasarorin a rayuwa.

    "A matsayinmu na musulmi, ya zama wajibi mu shiga tsakani. Sun kasance abokan juna, kuma sun yi abubuwa da dama a tare. Abin da ke faruwa a tsakaninsu a yanu abin takaici ne. Yanzu lokaci ya yi za a haɗa kai a zauna lafiya."

    Ya ce ko da ba za su haɗu a inuwar siyasa ɗaya ba, zai yi kyau su riƙa halartar sha'anin juna. "Mu ga Kwankwaso yana halartar auren ƴar Ganduje, shi ma Ganduje yana halartar auren ɗan Kwankwaso. Idan sun yi, a siyasa wannan ra'ayinsu ne, kowa ya yi nasa, amma shirya su, wannan nauyi ne a wuranmu."

  12. 'Tirelolin kayan agaji za su fara shiga Gaza'

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce ya ga motocin kayayyakin agaji da dama da suka kaasance a ajiye a Jordan, inda suke shirin shiga domin isar da kayayyakin zuwa Gaza.

    Kakakin asusun, Rosalia Bollen ta shaida wa BBC cewa suna fata hanyoyin da aka bi, za su taimaka wajen tsagaita wuta a yankin.

    Sai dai ta ce ko da ma an shigar da kayayyakin, raba su zai yi wahalar gaske, "saboda yadda yankin ya ɗaiɗaice."

    Ƙuncin rayuwa a Gaza ya yi tsanani, inda kusan kashi 91 na mutanen yankin suke fama da rashin abinci, kamar yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana.

    Ayyukan agaji zuwa Gaza sun yi kaɗan tun lokacin da aka fara yaƙin, kafin watan Oktoban 2023, aƙalla tirelolin kayayyakin agaji 500, ciki har da man fetur ne suke shiga Gaza a kuulum, amma tun bayan ɓarkewar yaƙin, sai aka fara samun koma-baya.

    A watan Oktoban 2024, alƙaluman Majalisar Ɗinkin Duniya sun nuna cewa aƙalla tirelolin kayayyakin agaji da suke shiga Gaza a kullum ba sa wuce 37, duk da cewa ba a haɗa da na fetur da tallafin masu zaman kansu ba.

  13. Matatar Dangote ta yi tasiri kan kasuwancin man fetur a duniya - OPEC

    OPEC

    Asalin hoton, Thinkstock

    Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur ta OPEC ta ce man fetur ɗin da matatar mai ta Dangote ke samarwa na matuƙar tasiri a kasauwar man fetur da yankin Turai.

    Mamatar man ta Dangote da ke iya samar da mai ganga dubu dari biyar, dai ta fara aiki ne a cikin watan Janairun bara, sannan ta fara samar da man fetur a cikin watan Satumba.

    Matatar ta dogara ne da samo ɗanyen mai daga ƙasashen wajen don samar da man fetur, wanda hakan ne ke tasiri kai-tsaye ga harkokin kasuwancin man a duniya.

    Sai dai a daidai lokacin da wasu ke mamaki, a nasa ɓangaren, Injiniya Yabagi Sani, wanda masani ne kan harkar makamashi ya ce kalaman na ƙungiyar ta OPEC bai zo musu da mamaki ba.

  14. Ɓangaren Fubara ya yi gaggawar kafa shugabancin riƙon ƙwarya na Rivers - PDP

    PDP

    Asalin hoton, PDP

    Jam'iyyar PDP a Najeriya ta ce, shugabacin jam'iyyar da ke biyayya ga tsohon gwamnan jihar Ribas Nyesom Wike, ta sani a matsayin shugabanin jam'iyyar a jihar ta Ribas.

    Jam'iyyar ta PDP ta ce duk da cewar an ɗaukaka ƙara kan hukuncin da kotu ta yi na sauke shugabanin jam'iyyar da ke Ribas, da ke biyyaya ga tsohon gwaman jihar, bai kamata ɓangaren gwamnan jihar su kafa wani shugabancin riƙon ƙwarya ba, kamata ya yi kowa ya dakata a jira hukucin kotu na gaba.

    Mataimakin kakakin jam'iyyar PDP na ƙasa, Ibrahim Abdullahi ne ya bayyana haka, inda ya ce kotun na gaba ne zai warware duk wani ƙullin da ke tattare da rikicin shugabancin jihar.

    Tun da farko dai, wata kotu ce ta rushe shugabannin jam'iyyar masu bibiya ga ministan Abuja, Nyesome Wike, wanda hakan ya sa ƴaƴan jam'iyyar na ɓangaren gwamnan jihar na yanzu, Simi Fubara suka sanar da kafa shugabancin riƙon ƙwarya.

  15. Najeriya da Nijar ƴan'uwan juna ne - Ambasada Sarki

    Nijar

    Asalin hoton, ORTN

    Ƙwararru da manyan masu ruwa da tsaki na ci gaba da yunƙurin sulhuntawa tsakanin Nijar da Nijeriya, manyan aminan ƙasashe kuma maƙwabtan juna a Afirka ta Yamma, da dangantakarsu ke daɗa tsami.

    Matakin na zuwa ne daidai lokacin da lamarin ke shiga shekara ta biyu.

    Babban mutum na baya-bayan nan da ya fito yake irin wannan kira, shi ne Ambasada Usman Sarki, wani tsohon babban jakadan Nijeriya da ya shafe gomman shekaru yana aiki a fannin diflomasiyya.

    Usman Sarki ya ce Nijar da Najeriya ƴanuwan juna ne, wanda hakan ya sa akwai buƙatar a samu maslaha a tsakani domin ci gaban yankin baki ɗaya.

  16. 'Boko Haram na amfani da jirgi mara matuƙi wajen tattara bayanai kan sojoji'

    Boko Haram

    Asalin hoton, Getty Images

    Masana harkokin tsaro, sun ce mayaƙan Boko Haram na amfani da jirgi mara matuƙi ne wajen tattara bayanai kan sojoji, saɓanin abin da wasu da hedikwatar tsaron ƙasar ke zargin wasu mutane da ba ƴan ƙasar bayanai.

    A cewar masana irin su Barista Audu Bulama Bukarti, mai bincike kan tsaro a yankin Sahel ya ce tsawon lokacin suna jan hakalin hukumomin tsaron ƙasar kan irin shirin da ƙungiyar Boko Haram ɗin ke yi, musamman amfani da jirgi mara matuƙi wajen kai hare-hare da tattara bayanai amma suka yi burus da hakan.

    Masanan dai na bayyana hakan ne bayan wata sanarwa da hedikwatar tsaron Najeriya ta fitar tana mai danganta yawaitar hare-haren da mayaƙan Boko haram ɗin ke yi ga wasu mayaƙan waje ne ke taimaka wa Boko Haram.

  17. Tattalin arzikin China ya ƙaru da kashi biyar

    China

    Asalin hoton, EPA

    Alƙalumman da hukumomi a China suka fitar sun nuna cewa ƙarfin tattalin arziƙin ƙasar ya ƙaru da ƙashi biyar cikin ɗari a shekarar da ta gabata, a wani yanayi na koma baya da aka kwashe gomman shekaru ba a gani ba, ko da yake adadin ya kai abin da gwamnati ke son ta cimmamawa.

    Ƙasar mafi girman tattalin arziƙi ta biyu a duniya ta koka kan tsawaita basussukan kadarori da kuma rage kashe kuɗaɗe. Sai dai bayanai na baya-baya nan sun nuna cewa a watan Disamba karon farko cikin wata 18 an samu daidaituwar farashin sabbin gidaje.

    Sai dai hukumomin Chinar sun yi gargaɗin cewa har yanzu tattalin arziƙin ƙasar na fuskantar ƙalubale da koma baya.

    Wakiliyar BBC ta ce hukumomin Chinar sun fahimci munin halin da ake ciki, shi ya sa suka ɗauki matakan da za su farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar.

  18. Gwamnatin tarayya ta ce za a kammala titin Abuja zuwa Kaduna a wata 14

    Abuja-Kaduna

    Gwamnatin Najeriya ta sake bayar da kwangilar gyaran babban titin Abuja zuwa Kaduna ga wasu kamfanoni uku bayan karɓe aikin daga kamfanin Julius Berger.

    Ministocin ayukka da watsa labarai na ƙasar ne suka sanar da hakan yayin ƙaddamar da sake aikin gyaran hanyar a ranar Alhamis a garin Tafa da ke jihar Neja.

    Gwamnatin ta ce an ba kamfanonin watanni 14 su kammala aikin, kamar yadda ministan yaɗa labarai na ƙasar, Alhaji Mohammed Idris ya bayyana.

    Ministocin sun ƙara da cewa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a shirye yake ya tabbatar an kammala aikin a wa'adin da ya bayar.

    "Idan aka kammala aikin, zai ɗauki shekara 50 zuwa 100," in ji ministan yada labarai.

  19. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'atu babbar rana daga nan sashen Hausa na BBC da muke kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sadarwa irin su Facebook da X da Instagram domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.