Hare-hare sun tilastawa MSF dakatar da wasu ayyukanta a Darfur

An tilastawa ƙungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières (MSF) rage tawagoginta tare da dakatar da duk wasu ayyuka a asibitin da ƙungiyar ke tallafawa a jihar Darfur ta tsakiya, ta ƙasar Sudan, sakamakon wani mummunan hari da aka kai a cikin cibiyar a daren asabar ɗin da ta gabata.
Harin ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya, sannan wasu biyar suka jikkata, ciki har da ma'aikacin ma'aikatar lafiya.
Wannan dakatar da ayyukan jinya na zuwa ne a lokacin ɓarkewar cutar kwalara.
MSF ta bayyana cewa ba za ta iya ci gaba da ayyukanta ba har sai dukkan ɓangarorin sun ba da tabbacin bayar da ingantaccen tsaro don kare ma'aikata da marasa lafiya.
Tun a ranar 1 ga watan Agusta, MSF ke jagorantar agajin gaggawa na yaƙi da cutar kwalara a asibitin Zalingei, inda ta kula da marasa lafiya 162 a cikin kwanaki 16 kacal, tare da haɗin gwiwar Ma'aikatar Lafiya ta Jihar.
Tuni dai cutar kwalara ta yio sanadiyar mutuwar mutane bakwai, kuma asibitin Zalingei ne kaɗai wurin da aka tanadar don kula da masu fama da munanan cututtuka a jihar Darfur ta tsakiya.




















