Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 27/12/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/12/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Abdullahi Bello da Isiyaku Muhammed

  1. Sai mun fatattaki ƴan Houthi za mu tsagaita wuta a Yemen - Netanyahu

    Netanyahu

    Asalin hoton, EPA

    Isra'ila ta yi gargaɗin cewa yanzu ta fara ɗaukar mataki kan ƴan Houthi a Yemen, waɗanda ke kai hare-hare kan Isra'ila da kuma jiragen ruwan dakon kaya a tekun Bahar Maliya.

    Gargaɗin ya fito ne daga Firaminista Benjamin Netanyahu, bayan da Isra'ila ta ƙaddamar da wasu hare-hare ta sama kan wasu wurare a ƙasar Yemen, wanda rahotanni suka sun kashe aƙalla mutum shida.

    Netanyahu ya ce, "mun ƙuduri aniyar kawar da wannan ɓangaren ta'addancin na ƙasar Iran. Za mu dage har sai mun cimma nasarar kammala aikin."

    A nasa ɓangaren, da yake bayyana yadda ya sha tsallake rijiya da baya, Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce tazarar mitoci kaɗan ne tsakaninsa da harin da aka kai a babban filin jirgin saman Sanaa, babban birnin ƙasar.

  2. Assalamu alaikum

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafin na kai-tsaye, muna muku barka da safiyar wannan rana ta Juma'a da fata kun wayi gari lafiya.

    A yau ma za mu ɗora, inda za mu cigaba da kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Idan kuka leƙa shafukanmu na sada zumunta za ku karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo.

    Ku kasance tare da mu.