Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya. 22/11/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Abdullahi Bello da Isiyaku Muhammed

  1. Netanyahu: Tarihin firaiministan Isra'ila da kotun manyan laifuka (ICC) ke nema

    Benjamin Netanyahu ya zamo shugaban ƙasa na huɗu wanda kotun hukunta manyan laifuka ta duniya (ICC) ta bayar da sammacin kamawa bisa zargin su da laifukan take haƙƙin bil'adama.

    Wannan ya sa ya shiga jerin shugabanni kamar Vladimir Putin na Rasha, da Omar al-Bashir na Sudan da kuma Muammar Gaddafi na Libya.

    Sammacin kama shi na da alaƙa ne da yaƙin da Isra'ila ta ƙaddamar a yankin Falasdinawa bayan harin da Hamas ta kai cikin Isra'ila a ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

    Zarge-zargen da ake yi wa Netanyahu sun haɗa da amfani da yunwa a matsayin makami kan fararen hula, da kisan gilla, da kuma ƙoƙarin kawo ƙarshen wata al'umma.

  2. Ana samun raguwar cutar ƙyandar biri a jamhuriyar Dimokradiyyar Congo

    Likitoci a cibiyar da aka samu ɓarkewar cutar ƙyandar biri a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo sun shaida wa BBC cewa an samu raguwar mutanen da ke kamuwa da cutar tun bayan da aka soma yi wa mutane rigakafinta a watan da ya gabata.

    Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta ce ba a samu ƙaruwar masu cutar ba amma ta yi gargaɗi cewa mutane ƙalilan ne ke zuwa a yi masu gwaji.

    Ƙwararru kan lafiyar al'umma a Afirka sun ce har yanzu cutar na bazuwa, ƙasashe 19 a nahiyar na samun ƙaruwar masu ɗauke da ita.

    Emmanuel Fikile, wani likita da ke aiki a kudu maso gabashin ƙasar yake cewa ba a samun masu fama da cutar kamar lokutan baya.

    Gaba a yau ne WHO za ta yi wani taro domin tsayar da matsaya kan ko har yanzu cutar ta Mpox barazana ce ga duniya.

  3. Alƙalin da ke shari'ar Trump ya sake ɗage shari'ar a karo na uku

    Alƙalin da ke sauraron shari'ar Donald Trump kan tuhumar da ake masa ta bayar da toshiyar baki, ya bayar da umarnin jinkirta yanke hukunci kan ƙarar har sai yadda hali ya yi sakamakon nasarar da ya samu ta sake lashe zaɓen shugaban Amurka.

    An tsara yanke wa zaɓaɓɓen shugaban ƙasar hukunci ranar Talatar makon gobe amma a yanzu, an ɗage.

    Lauyoyin Mista Trump sun ce ya kamata a yi watsi da shari'ar saboda rigar kariyar da shugaban ƙasa ke da ita inda suka ce hakan zai kawo cikas ga ƙoƙarinsa na tafiyar da mulki.

    A hukuncin na yau, alƙalin ya bayar da umarnin a gabatar da bukatar yin watsi da ƙarar nan da biyu ga watan gobe na Disamba.

  4. Babu wata ƙasa a duniya da ke da irin makamanmu - Putin

    Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ce zai ci gaba da yin gwajin da makamai masu linzami samfurin Oreshnik mai gudu fiye da sauti.

    Makamin mai linzami da aka harba ranar Alhamis an samu cikakkiyar nasarar yin gwajinsa, in ji Putin, inda ya ƙara da cewa babu wata ƙasa a duniya da take da irin makaman da kasarsa ke da su.

    Da yake magana yayin wata ganawa da jagororin tsaron ƙasar, Putin ya ce samar da sabbin makamai masu linzami dole ne bisa irin barazanar da suke fuskanta.

    Shugaban na Rasha ya kuma ce ba za a iya tare makaman masu linzami ba "sannan muna da irin waɗannan makaman kuma a shirye muke mu yi amfani da su", inda ya ƙara da cewa yanzu ya bayar da umarnin ƙera sabbin makaman babu ƙaƙƙautawa.

  5. An fitar da sabon daftari kan sauyin yanayi a taron Cop29

    Wani sabon daftarin yarjejeniyar sauyin yanayi ta duniya da aka cimma a taron sauyin yanayi na Cop29 ya ba da shawarar ƙasashe masu arziƙi su samar da dala biliyan ɗari biyu da hamsin duk shekara nan da 2035 domin taimaka wa ƙasashe matalauta su magance matsalar ɗumamar yanayi.

    An dai samu saɓanin ra'ayi a taron da ake a Azerbaijan kan ta inda kuɗaɗen za su fito inda ƙasashe masu tasowa ke neman a ƙara adadin kuɗin.

    Editan BBC kan yanayi Justin Rowlatt ke cewa ƙasashe masu tasowa sun ce suna buƙatar ƙarin kuɗi kuma sun yi ta jaddada cewa tiriliyoyi suke so ba biliyoyi ba.

    A yau ne aka tsara kammala taron na mako biyu amma mai yiwuwa ne a kai har ƙarshen mako ana gudanar da shi.

  6. Donald Tusk na Poland ya ce yaƙin Ukraine ya yi tsanani

    Firaiministan Poland ya yi gargaɗi cewa akwai babban haɗari da zai iya tasowa daga yaƙin da Rasha take a Ukraine.

    Donald Tusk wanda ke goyon bayan Ukraine, ya ce yaƙin ya yi tsanani.

    A jiya ne Rasha ta kai hari kan birnin Dnipro ta hanyar amfani da wani sabon makami mai cin matsakaicin zango.

    Fadar Kremlin tana barazanar sake ɗaukar fansa idan ba a saurari gargaɗinta ba game da abin da ta kira matakin Amurka da Birtaniya na ƙyale Ukraine ta harba makamai masu linzami cikin Rasha.

    Ƙungiyar tsaro ta Nato ta ce yin amfani da sabon makamin da Rasha ta yi ba zai hana ƙawayen Ukraine mara wa Kyiv baya ba.

  7. Jakadan Amurka a Sudan ya yi kira kan tsagaita wuta

    Jakadan Amurka a Sudan Tom Perriello ya yi kira da a kara matsa lamba don tattauna batun tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin da ke rikici da juna.

    Da yake magana da BBC bayan ziyararsa ta farko tun zama Jakada, Mista Perriello ya yi gargaɗi cewa yaƙin da aka shafe wata goma sha takwas ana gwabzawa babbar barazana ce ga tsaron yankin.

    Mista Perriello ke nan yake cewa abin da mutane ke son gani shi ne ƙasashe su daina tura makamai, su fara tura ƙarin abinci da magunguna, su kuma karkato da hankalinsu ga rikicin.

    Ya kuma yi kira ga rundunar sojin Sudan da dakarun RSF da su mutunta dokokin jin ƙai na duniya tare da ba da damar kai kayan agaji ga yankunan da rikicin ya fi shafa har da jihohin Khartoum da Gezira.

  8. Yadda kuɗin kirifto ke hauhawa a kasuwar duniya

  9. Mene ne makami mai linzami da ke ratsa nahiyoyi?

    Rasha ta yi amfani da ƙasar Ukraine a matsayin wani fage ko dandali na yin gwajin makamai - kamar dai yadda shugaban Ukraine ɗin Volodymyr Zelenski ya ce.

    "Dukkan wasu alamu da suka haɗa da gudu da nisan tafiya sun dace da makami mai linzami mai ratsa nahiyoyi" kamar dai yadda ya faɗa dangane da harin da aka kai birnin Dnipro da ke gabashi da safiyar Alhamis.

    Rasha ta ƙi cewa uffan dangane da harin da ƙasashen yammaci da dama suke tababar ko harin na makami mai linzami ne mai ratsa nahiyoyi.

    Idan har an tabbatar da cewa harin na makami mai linzamin ne mai ratsa nahiyoyi, to wannan ne zai zama hari irinsa na farko da aka kai da makamin da ake kira ICBM da ba a taɓa amfani da shi ba a duniya.

  10. 'Ba mu gamsu da ɗage babban taron ƙolin jam'iyyar PDP ba'

    Jam'iyyar PDP a shiyyar arewa ta tsakiyar Najeriya ta nuna rashin jin daɗinta game ba matakin da uwar jam'iyyar ta kasa ta ɗauka, na ɗage babban taron koli na jam'iyyar da aka shirya yi a Abuja a makon gobe.

    Jiga-jigan PDP sun ce wannan matakin ya saɓa wa kudin jam'iyyar.

    Tun bayan da aka naɗa Iliya Damagun a matsayin shugaban riƙo na jam'iyyar, PDP ta faɗa cikin rikici, a yayin da waɗansu 'yan jam'iyyar ke ƙoƙarin ganin an cire shi daga mukamin riƙon.

    Alhaji Yahaya Ability, shugaban jam'iyyar PDP a jihar Neja da ke tsakiyar Najeriya, ya shaida wa BBC cewa ɗage taron bai dace ba.

    " A watan da ya shige an sa za a yi wannan taron ranar 24 amma aka ɗaga zuwa 28 ga Nuwamba to amma shi ma an ɗage duk da cewa yanzu haka mu mun riga mun shigo birnin Abuja domin halartar wannan taro.

    Wannan ɗagawar ba a bayar da wani gamsashen bayani ba. Wai an ce an ɗaga ne domin a samu damar yin jana'izar matar gwamnan Akwa Ibom."

  11. Majalisar ta ƙayyade jari mafi ƙanƙanta ga kamfanonin dillancin wuta a Najeriya

    Majalisar wakilan Najeriya ta kawo shawarar ƙayyade naira biliyan ɗari biyar, a matsayin jari mafi ƙankanta da kamfanoni 11 da ke hidimar rarraba wutar lantarki na ƙasar, wato DisCos, za su mallaka, idan dai suna son ci gaba da gudanar da harkar.

    Hakan ya biyo bayan damuwar da ake ta nunawa, cewa kamfanonin raba wutar suna fama da ƙarancin kuɗin aiwatar da ayyukansu yadda kwalliya za ta biya kuɗin sabulu, har a ci ribar da ta kamata.

    Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar matsalar wutar lantarki sakamakon lalacewar cibiyar samar da wuta ta Najeriya ke ci gaba da yi.

  12. Rasha ta bai wa Koriya ta Arewa shingen kariyar sararin samaniya

    Mai bai wa Koriya ta Kudu shawara kan harkokin tsaro ya ce Rasha, a karon farko ta samar wa Koriya ta Arewa wasu makamai na kare sararin samaniyarta don samun taimakonta a yaƙin da take a Ukraine.

    Hakan na zuwa ne yayin da wasu hotunan tauraron ɗan'adam ke nuna alamun Rasha ta samar wa Koriya ta Arewa gangar mai sama da miliyan ɗaya tun watan Maris wanda hakan ya ci karo da takunkumin da ƙasashen duniya suka ƙaƙaba.

    Wannan ya kasance babbar fargabar Koriya ta Kudu ganin yadda Pyongyang ke ƙara nuna wa Rasha goyon baya a mamayar da ta yi wa Ukraine, wanda hakan kuma zai sa Shugaba Putin ya nuna godiyarsa ta hanyar miƙa mata makamai.

    Masu bincike sun bi sawun tankokin Koriya ta Arewa da suka ziyarci wata tashar mai ta Rasha da ke gabashin ƙasar har sau 43 a watanni takwas da suka gabata.

    A dalilin hakan ne suke ganin Rasha ta baiwa koriya ta Arewa fiye da gangar mai miliyan daya.

    Masana sun shaida wa BBC cewa babu shakka wannan man na matsayin ladan koriya ta Arewa na aika wa Rasha makamai, a yanzu kuma har da sojoji ,domin cigaba da yaƙi da Ukraine.

  13. Ana taƙaddama tsakanin Mbappe da PSG kan bashin albashi

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta Faransa ta yi watsi da buƙatar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta PSG kan ta sake duba umarnin da ta ba ƙungiyar umarnin cewa ta biya ɗan wasan gaban, Kylian Mbappe, bashin sama da dala miliyan 57.

    Wannan ya biyo bayan wata zazzafar taƙaddama tsakanin ɗanwasan wanda yanzu yake taka leda a ƙungiyar Real Madrid.

    Ɗanwasan yana ikirarin cewa yana bin PSG bashin albashi da wasu alawus, wanda ita kuma ƙungiyar ta ce ya amince zai yafe mata kuɗin idan ya tafi Real Madrid a matsayin kyauta.

    Matashin ɗanwasan ya koma Real Madrid ne a matsayin kyauta bayan kwantiraginsa da PSG ya ƙare.

    Ita dai PSG ta dage ba za ta biya bashin a yadda yake, wanda hakan ke nufin yanzu maganar a kotu za ta ƙare.

  14. Ƴan awaren Kamaru sun taƙaita sufurin motocin haya a yankin da suke da ƙarfi

    Ƙungiyar ƴan a-waren yankin rainon Ingilishi na Kamaru ta fitar da wani sabon umarni da ke hana motocin taksi masu fentin ruwan ɗorawa hawa titunan birnin Bamenda.

    A cewar ƙungiyar, launin ɗorawa alama ce ta gwamnatin Kamaru, don haka daga yanzu dole ne ƴan taksi su koma amfani da fentin fari da shuɗi.

    Shekara 7 ke nan da ɓarkewar rikicin, inda ƴan awaren suka dage sai sun ɓalle daga Kamaru.

  15. Nijar ta fara yunƙurin sake rubuta tarihinta

    Jamhuriyar Nijar ta fara ƙoƙarin sake rubuta tarihinta, wanda a yanzu ya fi ta'aƙalla da mulkin mallaka.

    Matakin na zuwa ne bayan shugaban mulkin soja, Janar Abdourahamane Tiani ya kafa wani kwamitin wucin gadi da aka ɗora wa alhakin wannan gagarumin aiki.

    Tun bayan juyin mulkin da Tiani ya yi Mohamad Bazoum, sabon shugaban na mulkin soji yake ta ɗaukar wasu matakai na rabuwa da abubuwa da suke alaƙanta ƙasar da Nijar.

    A watannin baya ne aka sauya sunan wasu manyan titunan ƙasar, inda suka cire sunayen Farasanci.

  16. Sojoji sun fatattaki Lakurawa daga Najeriya – Sanata Aliero

    Sanata mai wakiltar Kebbi ta tsakiya, Adamu Aliero, ya ce sojojin Najeriya sun samu nasarar fatattakar ƴan Lakurawa, inda suka tsallaka zuwa Nijar.

    A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a, Aliero ya ce an samu nasarar ne bayan ɗaukar matakin da ministan tsaro Abubakar Bagudu da babban hafsan tsaro da sauran masu ruwa da tsaki suka ɗauka, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

    Aliero ya ce, "mun faɗa wa ministan cewa idan aka yi sakaci da ƴanta'addan Lakurawa, za a iya maimaita abin da ya faru a arewa maso gabas a arewa maso yamma. Yaƙi ne da za a iya gamawa a kwana biyar, amma idan aka yi sakaci, lamarin zai ƙazance saboda yankin arewa maso yamma ya fi yawan mutane kuma ya fi arziki da ma girman ƙasar noma da kiwo.

    "Amma kun san da sojoji suka zo a ranar Talata (12 ga Nuwamba) sun samu nasarar fatattakarsu zuwa Jamhuriyar Nijar?"

    Ƴan Lakurawa sun kashe mutane da dama a jihar Kebbi, lamarin da ya sa Sanata Aliero da sauran ƴan majalisar jihar suka kai ziyara a ƙananan hukumomin Argungu da Augie domin gane wa idonsu irin ɓarnar da suke yi.

  17. Sojoji sun kashe ƴanbindiga a Katsina

    Hukumomi a jihar Katsina sun ce wani harin sojojin sama ya yi sanadin hallaka ƴan fashin daji sama da 100 da safiyar jiya Alhamis a ƙauyen Shawu na ƙaramar hukumar Faskari.

    Bayanai sun ce lamarin ya faru ne bayan wani shiri da ƴanbindigar suka yi na kai wa jami'an tsaro hari a yankin.

    Nasiru Ma’azu shi ne kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Katsina, ga kuma tabbatar da faruwar lamarin a zantawarsa da BBC.

  18. IPOB: Najeriya na so a miƙa mata Simon Ekpa

    Hedkwatar tsaron Najeriya ta nuna farin cikinta da kama Simon Ekpa wanda jagoran haramtacciyar ƙungiyar IPOB ne a ƙasar Finland.

    Babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa ne ya bayyana hakan, bayan hukumomin Finland sun sanar da cika hannu da shi.

    Cikin wani saƙo da kakakin ma'aikata tsaron ƙasar, Manjo Janar Tukur Gusau ya aike wa BBC ya ce babban hafsan tsaron ƙasar ya ce yana fatan kamen ya zama wani mataki na tisa ƙeyar Mista ekpa zuwa Najeriya don ya fuskanci shari'a.

    A ranar Alhamsi ne hukumomin Finland suka kama Simon Ekpa tare da aika shi gidan yarin ƙasar, bayan gurfanar da shi a kotu, kan zargin tunzura mutane su aikata ayyukan ta'addanci.

  19. Atiku ya gargaɗi Tinubu kan yawan ciyo bashi

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya ce yawaitar ciyo basussuka da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi zai ƙara jefa tattalin arzikin Najeriya cikin ƙunci.

    Tsohon ɗantakarar na PDP ya kuma soki yadda majalisar dokoki ke amincewa da buƙatar ciyo basussukan, waɗanda a cewarsa suke ƙara jefa ƙasar cikin ƙangin bashi.

    Atiku ya bayyana haka ne a wani rubuta da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce, "rahoton da bankin duniya ya fitar kwanan nan, wanda ke nuna cewa Najeriya ce ƙasa ta uku da ta fi cin bashi daga hukumomin kuɗi na duniya abin damuwa ne.

    "Rahoton ya fito ne a daidai lokacin da gwamnatin ƙasar ta aike da wani buƙatar sake ciyo wani bashin na naira triliyan 1.7 saboda cike giɓin kasafin kuɗin 2024. Abin da zai ƙara ɗaga hankali a game da bashin ma shi ne kasancewarar a kasafin kuɗin, an kasafta darajar dala ɗaya a kan naira 800, alhali yanzu dala ta kai naira 1,600."

    Ya ƙara da cewa Najeriya na ƙara nutsewa a cikin bashi, "sannan majalisar dokoki suna taimakawa. Tinubu ya bayyana a watan Yuli cewa hukumar tattara haraji da kwastam sun tara kuɗin shiga da ba a taɓa tarawa ba. To me ya sa ake cin bashin? akwai wani abu da suke ɓoyewa ƴan Najeriya."

    Atiku ya ƙara da cewa yawan cin bashin yana ƙara takurawa tattalin arzikin.

  20. Amurka ta yi kiran matsa lamba don kawo ƙarshen yaƙin Sudan

    Jakadan Amurka na musamman a Sudan, Tom Perriello, ya yi kiran matsa lamba domin kawo ɓangarori biyu da ke rikici da juna a ƙasar kan teburin sulhu.

    Yayin da yake magana da BBC bayan ziyararsa farko zuwa ƙasar tun naɗa shi muƙamin, Mista Perriello ya yi gargaɗin cewar yaƙin na tsawon wata 18 ka iya haifar da barazanar tsaro a yankin tsakiyar Afirka.

    Jakadan na musamman ya kuma buƙaci waɗanda ya kira ''masu rura wutar rikicin a bayan fage'' su daina aika makamai zuwa ƙasar tare da kiran ƙasashen duniya su ƙara jajircewa wajen kawo ƙarshen yaƙin.

    Haka kuma mista Perriello ya yi kira ga rundunar sojin ƙasar, da dakarun RSF su martaba dokokin jin ƙai na duniya, domin bayar da damar shigar da kayan agaji zuwa yankunan da yaƙin ya ɗaiɗaita, ciki har da birnin Khartoum da jihar Gezira.