Cambodia ke saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta - Thailand

Asalin hoton, Getty Images
Thailand ta zargi Cambodia da saɓa yarjejeniya tsagaita wuta da aka amince bayan kwana biyar na rikicin kan iyaka tsakaninsu.
Thailand ta ce Cambodia ta kai hare-hare wurare da dama jim kaɗan bayan yarjejeniyar tsagaita wutar ta fara aiki, wanda ya sa sojojin Thailand suka mayar da martani.
An bayar da rahoton cewa kura ta lafa a yanzu, amma an dage tattaunawar da ya kamata kwamandojin soji su yi.
A jiya Litinin ne aka amince da yarjejeniyar tsakanin Thailand da Cambodia a tattaunawar da Malasia ta jagoranta





